Aminiya:
2025-04-19@21:17:21 GMT

Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara

Published: 27th, March 2025 GMT

Kantoman Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya dakatar da dukkanin masu riƙe da muƙaman siyasa da jami’an gwamnatin jihar nan take.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, Ibas, ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bisa izinin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata ranakun hutun sallah Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji

Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sakatare na Gwamnatin jihar, Shugaban Ma’aikata, Kwamishinoni, shugabannin hukumomi, da masu ba da shawara na musamman.

Ya umarci duk waɗanda abin ya shafa da su miƙa ragamar ayyukansu ga sakatarorin ma’aikatunsu.

Ya ce hukumomin da babu sakatare, sai a bai wa babban darakta mafi girma ko shugaban gudanarwa.

Wannan umarni ya fara aiki daga ranar Laraba, 26 ga watan Maris, 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa Muƙaman Siyasa umarni

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana

Gwamnatin Jihar Yobe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni  ta sayo ton 2,000 na hatsi iri-iri domin ƙarfafa samar da abinci da kuma tabbatar da shirin tunkarar kakar bana a matsayin gudun ko ta kwana.

A cikin wata sanarwa da Yusuf Ali, mai bada shawara ta musamman kan harkokin dabarun sadarwa na zamani (SSA) ga gwamna Buni ya ce,  Kwamishinan ma’aikatar noma da albarkatun ƙasa, Ali Mustapha Goniri, ya kai ziyarar duba irin hatsin a shagunan bunƙasa noma na jiha  da ke kan titin Gujba da ke Damaturu.

’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista ISWAP sun ruguza gadar Mandafuma a Borno

Da yake zantawa da manema labarai a yayin ziyarar, Ali Mustapha ya bayyana kyakkyawan fata game da shirin, inda ya jaddada cewa za a raba hatsin ga jama’ar Yobe a cikin gaggawa ko kuma lokacin bazara domin rage matsalar ƙarancin abinci.

Baya ga hatsin, Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnati ta sayo nau’o’in sinadarai iri-iri domin tallafa wa manoman rani da kayan lambu.

Ya kuma bayyana shirin raba irin rogo ga manoma a fadin jihar, da nufin farfaɗo da noman na rogo lura da amfanin da ake yi da ita ta fuskoki iri-iri na abinci har ma da sarrafa ta da ake yi ya zuwa garin fulawa don yin abubuwa da ita.

Kwamishinan ya yabawa gwamnatin Gwamna Mai Mala Buni, bisa jajircewa da goyon baya da take bayarwa wajen bunƙasa harkar noma a Jihar Yobe.

Tawagar binciken ta haɗa da babban sakataren ma’aikatar, Barista Muhammed Inuwa Gulani da daraktoci da sauran jami’an ma’aikatar.

Wannan shiri ya ƙara jaddada ƙudirin gwamnatin Jihar Yobe na inganta samar da abinci da kuma baiwa manoma damar bunƙasa harkokin su na noma da nufin samar da ishasshen abinci a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu
  • Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo
  • Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano