Aminiya:
2025-03-30@13:10:04 GMT

Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara

Published: 27th, March 2025 GMT

Kantoman Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya dakatar da dukkanin masu riƙe da muƙaman siyasa da jami’an gwamnatin jihar nan take.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, Ibas, ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bisa izinin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata ranakun hutun sallah Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji

Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sakatare na Gwamnatin jihar, Shugaban Ma’aikata, Kwamishinoni, shugabannin hukumomi, da masu ba da shawara na musamman.

Ya umarci duk waɗanda abin ya shafa da su miƙa ragamar ayyukansu ga sakatarorin ma’aikatunsu.

Ya ce hukumomin da babu sakatare, sai a bai wa babban darakta mafi girma ko shugaban gudanarwa.

Wannan umarni ya fara aiki daga ranar Laraba, 26 ga watan Maris, 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatarwa Muƙaman Siyasa umarni

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja

Rahotanni daga Najeriya na cewa mutane 20 ne suka mutu sakamakon hatsaniyar da aka samu tsakanin sojoji da masu jerin gwanon ranar Kudus ta duniya a Abuja fadar mukin Najeriya.

Hotunan faifan bidiyo sun nuna yadda masu zanga-zangar ke neman mafaka yayin da karar harbe-harbe ke kara kamari a kusa da su.

An ce an kai gawarwakin mutanen goma sha hudu zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Ana gudanar da tattakin ranar Qudus ta duniya duk shekara a ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan domin nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja
  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
  • Kisan ‘Yan Arewa 16 A Jihar Edo: Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Nemi Adalci
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki
  • Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar
  • Kwankwaso Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Arewa A Edo, Ya Buƙaci A Yi Adalci
  • Dalilin Da Ya Sa Ɗanyen Man Da Ake Haƙowa A Ribas Ya Ragu
  • Gwamnatin Amurka Tana Shirin Dakatar Da Bada Kudaden Tallafi Don Samar Da Wasu Magunguna