HausaTv:
2025-04-19@17:10:40 GMT

Sudan : Janar al-Burhan Ya Shelanta ‘yantar Da Birnin Khartoum

Published: 27th, March 2025 GMT

Babban hafsan sojojin Sudan Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya shelanta  ‘yantar da Khartoum Babban birnin kasar.

Wannan na zuwa ne bayan da tun da farko ya sanar da cewa dakarunsa sun kwato filin jirgin saman babban birnin, wuri mai matukar mahimmanci daga hannun dakarun ‘yan tawaye na RSF.

“An ‘yantar da Khartoum, an gama,” in ji shugaban na Sudan daga fadar shugaban kasa a wani jawabi da aka watsa a gidan talabijin na kasar.

Kazalika, wata sanarwa da sashen watsa labarai na majalisar rikon kwarya mai mulkin kasar ta fitar, ta ce Al-Burhan ya sauka a filin jirgin sama na kasa da kasa dake birnin Khartoum ta jirgi mai saukar ungulu a jiyan, jirgin da ya zamo na farko da ya sauka a filin, tun bayan barkewar tashin hankali a watan Afrilun shekarar 2023.

Daga nan ne kuma ya duba sassan rundunar sojin gwamnati dake tsaron filin jirgin kafin ya wuce zuwa fadar gwamnati.

Tun daga farkon shekarar 2024, dakarun sojin gwamnati na SAF ke ta kwace sassan kasar daban daban, musamman a birnin Omdurman na arewacin Khartoum, inda suka kwace kaso mai yawa na birnin, lamarin da ya karfafa ikonsu sama da na dakarun RSF a yankin.

A ranar Juma’a data gabata, sojojin na sudan sun ayyana kwace iko da fadar gwamnati, da wasu muhimman ofisoshin gwamnatin kasar dake Khartoum, wuraren da a baya suka kasance muhimman sassa da dakarun RSF ke rike da su a birnin na Khartoum.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing
  • Amurka Ta Kaddamar Da Sabbin Hare-Hare Kan Garuruwan Sana’a, Sa’adah Da Al-Jawf Na Kasar Yemen
  • Sojojin Sudan Sun Kashe ‘Yan Tawayen Kasar Ciki Har Da Manyan Kwamandojinsu A Birnin El Fasher
  • Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome
  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
  • Babban Jami’in Diblomasiyyar Iran Ya Je Birnin Mosco Don Isar Da Sakon Imam Khaminae Ga Putin
  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • ‘Yan tawayen Sudan sun kafa tasu gwamnati