HausaTv:
2025-03-30@13:19:32 GMT

Sudan ta Kudu : Ana tsare da Riek Machar a wani gida

Published: 27th, March 2025 GMT

Bayanai daga Sudan ta kudu na nuni da cewa ana tsare damataimakin shugaban kasar na farko Riek Machar a wani gida, lamarin da MDD ta nuna matukar damuwa na yiwuwar komawar kasar wani yakin basasa.

Rahotanni sun ce a yammacin jiya Laraba jami’an tsaron Sudan ta Kudu sun tsare Riek Machar, kamar yadda kakakinsa ya sanar.

Ba a fayyace ainihin dalilin wannan tsarewar da kuma tasirinta ga dorewar yarjejeniyar zaman lafiya da aka rattabawa hannu a shekarar 2018 ba.

Tun a farkon watan Maris ne dai ake ta rade-radin kame Riek Machar, lokacin da rikicin yankin Upper Nile da ke arewa maso gabashin kasar ya kai ga kame wasu jami’an jam’iyyarsa a Juba.

tsare Mista Machar madugun ‘yan adawa na kasar na jefa shakku sosai kan shirin samar da zaman lafiya a Sudan ta Kudu a cewar masana.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Riek Machar

এছাড়াও পড়ুন:

An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara ta kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ake kira Ɗan Mudale da ya addabi mazauna yankin Tsafe da kewaye.

Rundunar ta ce a jiya Alhamis ne ta daƙile wani harin ’yan bindiga a ƙauyen Keta da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta jihar.

’Yan sanda sun haramta hawan Sallah a Kano Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar ya fitar a Gusau, babban birnin jihar.

A cewar DSP Yazid, a yayin daƙile harin ne ’yan sanda suka kashe gomman ’yan bindigar ciki har da Ɗan Mudale wanda ya addabi al’ummar yankin.

Ya ce rundunar haɗin gwiwa da ta haɗa da ’yan sanda da askarawa da kuma mafarauta ce ta yi karon batta da ’yan ta’addar da aka riƙa musayar wuta.

Sai dai ya bayyana takaicin cewa wani jami’in ɗan sanda daya da askarawa huɗu da kuma mafarauta sun bayar da ransu a yayin artabun.

Sanarwar ta ce a halin yanzu wasu mafarauta biyu na karɓar magani a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Gusau.

Kazalika, rundunar ’yan sandan ta ƙara jaddada ƙudirinta na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

Ta yi kira ga mazauna da su riƙa gaggauta miƙa mata rahoton duk wani motsi da su aminta da shi ba domin a ɗauki matakin da ya dace.

Mutuwar Ɗan Mudale ne zuwa bayan kashe Kachalla Isuhu Yellow, wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ke sahun waɗanda suka jagoranci kitsa harin da aka kai jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja shekaru biyu da suka gabata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi
  • Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara
  • Aminu Bayero ya soke hawan Sallah
  • Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa