HausaTv:
2025-03-30@13:19:32 GMT

Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian

Published: 27th, March 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi kira ga al’ummar kasar da su nuna hadin kai a yayin bukukuwan ranar Kudus ta duniya wato ranar JUma’ar kashe ta watan Ramadana da ke gabatowa, yana mai jaddada cewa hakan zai nuna matukar goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ga al’ummar Falastinu.

Pezeshkian, ya bayyana hakan ne a yayin taron majalisar ministocin kasar na farko sabuwar shekarar kalandar farisa, inda yake cewa “Ina fatan tare da halartar al’ummar kasar, za a gudanar da ranar Kudus mai daraja, kuma a wannan rana al’umma za su nuna hadin kai ga duniya.

Ranar Kudus ta duniya dai marigayi Imam Khumaini ne ya ayyana ta kuma ana gudanar da ita a kowace shekara a ranar Juma’ar karshe ta azumin watan Ramadan domin nuna goyan baya ga al’ummar falasdinu.

Ta kasance wani gangami na duniya ga musulmi da masu neman ‘yanci a wajen bayyana goyon bayansu ga al’ummar Falastinu tare da yin Allah wadai da mamayar da gwamnatin Isra’ila ke yi wa yankunan Falastinawa da kuma cin zarafin da take yi wa masallacin Kudus.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ga al ummar ranar Kudus

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Gudanar Da Faretin Jiragen Ruwa A Tekun Farisa Da Kuma Tekun Caspian Don Raya Ranar Kudud Ta Duniya

Jiragen ruwan yaki na dakarun juyin juya halin musulunci  IRGC a nan Iran, kanana da manya-manya, har’ila yau da na masu sa kai sun gudanar da faretin jiragen ruwan yaki don raya ranar Kudus ta duniya kwana guda kafin ranar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto dubban  jiragen yaki da na masu sa kai a tekun Farisa da ke kudancin kasar da kuma tekun Caspian da ke arewacin kasar suna jerin gwano a cikin ruwayen yankunansu don raya wannan ranar.

Dakarun IRGC sun gudanar da wannan atisai ne a jiya Alhamis, don nuna goyon bayansu ga Falasdinwa musamman a Gaza, wadanda a halin yanzu, sojojin HKI sun yi masau kawayya, sun hana shigowar abinda da abinsha  cikin yankin sama da wata gusa, sannan suna binsu suna kashewa.

Majiyar dakarun IRGC ta bayyana cewa sama da jiragen ruwa da kwale-kwale kimani 3,000 ne suka fito don tallafawa falasdinawa musamman a Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan, wadanda sojojin yahudawa suka kashewa a ko wace rana.

Labarin ya kara da cewa, a kudancin kasar an baje kolin katafaren jirgin ruwa mai daukar jirage yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa, mai sun a ‘shahida beheshti’, jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa suna sauka su kuma tashi a kan wannan jirgin yakin.

HKI dai wacce take samun tallafin kasashen yamma musamman Amurka suna mamaye da kasar Falasdinu fiye da shekaru 70 a halin yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  •  Ayatullah Khatami: Jerin Gwanon Ranar Qudus Rana Ce Mai Matukar Muhimmaci A Musulunci
  • Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025
  • Jerin Gwanon Ranar Kudus Na Ci Gaba Da Gudana A Kasashen Duniya
  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a
  • Jagora Ya Yi Kira Ga Iraniyawa Su Fito Don Gudanar Da Gagarumar Zanga-Zargar Ranar Kudus Ta Duniya
  • Iran Ta Gudanar Da Faretin Jiragen Ruwa A Tekun Farisa Da Kuma Tekun Caspian Don Raya Ranar Kudud Ta Duniya
  •  Sojojin Iran: Gwagwarmaya Ce Kadai Hanyar Warware Matsalar Falasdinu