Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu
Published: 27th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi kira hadin kan kasashen duniya domin nuna goyon baya ga Falasdinu gabanin ranar Kudus ta Duniya.
Kungiyar ta yi kira da a samar da hadin kai a kasashen duniya a ranar Juma’a da Asabar da Lahadi masu zuwa domin nuna goyon baya ga Gaza da Kudus, yayin da Isra’ila tare da goyon bayan Amurka ke ci gaba da yakin kisan kare dangi da suke yi wa Falasdinawa.
A cikin sanarwar da ta fitar, Hamas ta yi kira da a gudanar da gagarumin jerin gwano na hadin gwiwa a dukkan birane da manyan birane na duniya.
“Muna kira ga daukacin al’ummar Falasdinu, kasashen Larabawa da na Musulunci, da dukkan al’ummarmu masu son ‘yanci na duniya da su fito a ranar Juma’a, Asabar, da Lahadi mai zuwa don kare Gaza, Quds, da masallacin Aqsa, da goyon bayan juriyar jama’armu, da yin tir da laifuffuka da tsare-tsare na gwamnatin mulkin mallaka a kan kasarmu, mutanenmu, da wurarenmu masu tsarki da ake yi a Gaza.” Inji Hamas
Hamas ta kuma yi kira da a ci gaba da matsin lamba ga gwamnatin Isra’ila don kawo karshen zalunci da kisan kiyashi ga Palasdinawa, Har ila yau sanarwar ta yi kira ga masu hudubar sallar Juma’a da su sadaukar da jawabansu na wannan Juma’a kan batun Falastinu, domin kwadaitar da al’ummar musulmi wajen karfafa goyon bayansu ga al’ummar Palastinu da suke fafutukar kare kasarsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu
Kasashen Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu domin cin moriyar juna a matsayinsu na makobta.
Wannan bayyanin ya fito bayan tattaunawa data wakana tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen biyu a birnin Yamai bayan kwashe watanni ana takaddama.
Yayin ziyarar da ministan harkokin wajen Najeriya ya kai Nijar an gudanar da wani babban taro tsakanin shugabannin diflomasiyyar kasashen biyu don sake farfado da hanyoyin hadin gwiwa a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki da tsaro.
Ministan harkokin waje da hadin gwiwa na Nijar Bakary Yaou Sangaré da takwaransa na Najeriya Yusuf Maitama Tuggar sun gana a ranar 16 ga ga watan nan, lamarin dake nuni da wani gagarumin sauyi na dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu da ta yi tsami tsawon watanni biyo bayan juyin mulkin da ya faru a ranar 26 ga watan Yulin 2023.
bangarorin biyu sun kuma tattauna kan barazanar ta’addanci a kan iyakokinsu, inda suka jaddada aniyarsu ta hada karfi da karfe wajen yakar kungiyoyin da ke dauke da makamai da ke kawo cikas wajen aiwatar da dukkanin shirye-shiryen ci gaba a kasashen biyu cikin shekaru da dama. Inda suka bukaci ma’aikatun tsaron kasashen biyu da su ci gaba da hadin gwiwa a fannin tsaro.
Dangantaka tsakanin kasashen biyu da ke makwabtaka da juna ta tabarbare ne a lokacin da Najeriya ta taka muhimmiyar rawa wajen daukar matakan kakabawa Yamai takunkumin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS ta kakabawa kasar, wanda hakan ya bata dangantakar da ke tsakaninsu.