Sarkin Kano Na 15 Ya Soke Hawan Daba Saboda Matsalar Tsaro
Published: 27th, March 2025 GMT
Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke bikin Sallar Eid-el-Fitr Durbar, saboda matsalar tsaro da ya sa aka dakatar da shirye-shiryen.
Sarkin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai a fadarsa ta karamar hukumar Nasarawa da ke Kano.
Ya kuma jaddada cewa zaman lafiya a tsakanin jama’a ya fi muhimmanci fiye da bikin Durbar.
Bayero ya yi nuni da cewa manyan Malaman addinin Musulunci da dattawa da masu ruwa da tsaki da ‘yan majalisarsa suka bada shawarar a soke bikin domin a samu zaman lafiya.
Alhaji Aminu Ado Bayero ya bukaci al’ummar Kano da su yi amfani da lokacin bukukuwan Sallah wajen ziyartar ‘yan uwa da abokan arziki, tare da shaida yadda bikin Sallah cikin kwanciyar hankali da lumana.
Ya yi addu’ar Allah ya jikanmu da rahama albarakcin wannan watan na Ramadan tare da fatan al’ummar Kano za su kasance cikin masu samun gafara da rahama.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarki na 15
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su, a wani samame da ta gudanar cikin gaggawa tare da tabbatar da ganin an dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Yazid Abubakar ya fitar, ya ce a ranar 16 ga Afrilu, 2025, da misalin karfe 1:45 na rana, tawagar hadin guiwa da ta kunshi jami’an ‘yan sanda da kuma jami’an kare hakkin jama’a (CPG) suna sintiri a kan babbar hanyar Anka-Gummi, inda suka gano wata mota samfurin Peugeot 206 da suka yi garkuwa da su a gefen hanya.
A cewar sanarwar, ba tare da bata lokaci ba, tawagar jami’an tsaro ta fara gudanar da wani bincike na hadin gwiwa, wanda ya kai ga ceto mutane shida da aka yi garkuwa da su, yayin da mutanen da aka ceto suka koma ga iyalansu.
Ta ce kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya yabawa ‘yan sandan bisa gaggauwa da daukar matakin da suka dauka.
Ya nanata kwazon rundunar tare da sauran jami’an tsaro na ganin an ceto duk wadanda aka sace tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar.
CP Maikaba ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su sanya ido tare da gaggauta kai rahoton duk wani abin da ba su gane ba ga jami’an tsaro mafi kusa da su domin kawo dauki cikin gaggawa.
Sanarwar ta kuma jaddada cewa, rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta wargaza maboyar barayi da kuma dawo da zaman lafiya mai dorewa a jihar.
REL/AMINU DALHATU.