Kungiyoyin kwadagon Najeriya NLC da TUC a jihar Zamfara sun bayar da wa’adin kwanaki 14 ga gwamnatin jihar, inda suka bukaci da a kawo karshen kura-kuran da aka samu wajen aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000.

 

An sanar da wa’adin ne a wani taron manema labarai a Gusau bayan wani taron gaggawa da kungiyoyin kwadago suka yi.

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban kungiyar NLC na jihar Zamfara, Malam Sani Halliru, ya bayyana rashin jituwar da ake samu wajen biyan albashin watan Maris a matsayin abin bakin ciki da damuwa ga ma’aikatan gwamnati.

 

“Ya zama dole mu kira wannan taron manema labarai saboda mun ji takaicin yadda gwamnatin jihar ke aiwatar da mafi karancin albashi,” in ji Halliru.

 

Ya kara da cewa tun da farko gwamnatin jihar ta kafa kwamitin da zai sa ido a kan yadda za a aiwatar da sabon albashin tare da tabbatar wa ma’aikata cewa za a fara aiki a watan Maris. Sai dai ya lura cewa albashin watan Maris da aka biya a baya-bayan nan ya gaza yadda ake tsammani.

 

“Wasu ma’aikata sun samu karin Naira 3,000 kacal, yayin da wasu suka samu N4,000, N5,000, ko kuma akalla Naira 7,000. Har ma fiye da haka, an cire wasu ma’aikatan ba bisa ka’ida ba daga cikin albashin ma’aikata.” Ya kara da cewa.

 

Malam Sani Haliru ya kuma bayyana lamarin a matsayin cin amana, ya kuma yi gargadin cewa, idan gwamnati ta gaza magance wadannan matsalolin nan da makonni biyu, kungiyoyin za su dauki mataki.

 

Shi ma da yake jawabi, Shugaban TUC, Sa’idu Mudi, ya koka kan yadda har yanzu Zamfara ce jiha daya tilo da ba ta fara aiwatar da mafi karancin albashi na N70,000.

 

“Dukkan shugabannin kwadago da ma’aikata a jihar sun ji takaicin gazawar gwamnati wajen cika alkawarin da ta dauka.

 

A cewar Mudi sun ji takaicin kwamitin da aka nada domin aiwatar da sabon albashin yaki yin aikin da ya dace.

 

Ya yi zargin cewa da gangan wasu mutane a cikin gwamnati ke yin zagon kasa wajen aiwatar da aikin tare da yin kira ga Gwamna Dauda Lawal da ya kaddamar da bincike kan lamarin tare da daukar matakin da ya dace.

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Duk wani ci gaba ya dogara da muhimmancin da Washington za ta ba tattauwar  

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce duk wani ci gaba da za’a samu a tattaunawa da Amurka ya dogara ne da muhimmancin da Washington ta ba tattaunawar.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, Araghchi ya ce barazana da kuma takunkumin da Amurka ke kakaba wa Iran, ya kara haifar da shakku game da aniyar Washington na neman hanyar diflomasiyya.

“Don ci gaba a kan wannan tafarki dole ne dayan bangaren ya nuna kyakkyawar niyya cewa da gaske ya ke,” in ji shi, kafin ya ce: “Iran, a matsayinta na mamba a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT), dole ne ta ci moriyar makamashin nukiliya don dalilai na zaman lafiya.”

Ministan na Iran ya kara jaddada cewa, domin cimma daidaito, da kuma dawwamamiyar yarjejeniya, tilas ne dukkan bangarorin su kaurace wa duk wasu bukatu da suka saba wa yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya.

Abbas Araghchi ya kuma yi tsokaci kan gazawar Amurka wajen cika alkawuran da ta dauka karkashin yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015, yana mai jaddada cewa dole ne sauran bangarorin su ba da tabbacin dage takunkumin da aka kakaba iran.

A nasa bangaren babban sakataren MDD ya jaddada muhimmancin ci gaba da tattaunawa har sai an samu sakamako.

Mr. Guterres ya kuma yaba da sabbin hanyoyin da ministan harkokin wajen Iran ya bi wajen bayyana abubuwan da ke faruwa a tattaunawar ta tsakanin Iran da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Taron Dangi Kan Kasar Yemen
  • Za A Gudanar Da Taron Tallata Fim Din “Red Silk” A Moscow
  • Kwankwaso: Abba ya mayar wa Baffa Bichi martani
  • Lakurawa: Yadda mafarauta 13 suka gamu da ajalinsu a Sakkwato
  • Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato
  • An kammala Bada Horo Ga Matan Sojojin Runduna Ta 8 Da Ke Sakkwato
  • Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • An Share Filin Noma Kadada 100 Don Karfafa Matasa Su Yi Noma A Babura Jihar Jigawa
  • Kiwon Lafiya: Jihar Kwara Ta Bayyana Yadda Karancin Likitoci Ke Kawo Mata Cikas
  • Araghchi : Duk wani ci gaba ya dogara da muhimmancin da Washington za ta ba tattauwar