Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-19@21:12:01 GMT

Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa

Published: 27th, March 2025 GMT

Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa

Gwamnatin jihar Kwara ta gargadi mazauna jihar kan yin gine-gine a kan bututun ruwa a fadin jihar.

 

Kwamishinan Albarkatun Ruwa na Jihar, Usman Yunusa Lade, ya yi wannan gargadin a lokacin da ya kai ziyarar duba aikin gyaran babban bututun ruwa dake Flower Garden, a Ilorin.

 

Kwamishinan, wanda ya samu wakilcin Sakatariyar Dindindin, Misis Christiana Asonibare, ta ce “kamar gine-gine, masallatai, coci-coci da shaguna a kan bututun ruwa da jama’a ke yi yana da illa ga samar da isasshen ruwa a fadin jihar.

 

Yunusa -Lade ya yi kira ga daukacin mazauna yankin da su kara kaimi ga kokarin gwamnati ta hanyar yin la’akari da bututun ruwa kafin a gina wani gini domin kaucewa lalata bututun ruwa da hana ruwa gudu ga al’umma.

 

A nasa bangaren babban Injiniya mai kula da aikin gyaran bututun da aka gyara a lambun Flower, Bamidele Idowu, ya tabbatar da cewa an kammala gyaran kuma za a gudanar da gwajin domin tabbatar da cewa ba a samu matsala ba.

 

Idowu ya bada tabbacin cewa yankunan da suka hada da Flower Garden, Lajorin, Offa Road, Sabo-Oke, Amilengbe, Adualere, Isale-koko, Oja-Gboro, da Ipata da dai sauransu za su ci gajiyar kammala gyaran da zarar an fara aikin turo ruwa.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Ruwa bututun ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas

Jawabin shugaban majalisar, ya biyo bayan dambarwar hankalin al’ummar kasar ne, bayan shelar ranar 18 ga watan Maris da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi na ayyana dokar ta-baci na tsawon wata shida a Jihar Ribas. Matakin ya zo ne daidai lokacin da rikicin siyasa ke kara kamari, inda aka dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara tare da rusa majalisar dokokin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • Gwamnatin Yobe ta sayo hatsi don tunkarar kakar bana
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Mabiyan Bana A Jigawa
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka