Aminiya:
2025-03-30@14:35:44 GMT

Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a Kebbi

Published: 27th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin Lakurawa ne, sun kai har iyakar Bachaka da ke Ƙaramar Hukumar Argungu a Jihar Kebbi, inda suka kashe jami’an Kwastam biyu da wani mazaunin garin.

Harin ya faru ne kwana guda bayan da dakarun tsaro suka kashe wasu dakarun Lakurawa a yankin.

Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD

Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi, ta tabbatar da faruwar harin, inda ta ce ba a tantance sunayen jami’an Kwastam da aka kashe ba.

“Eh, an kai hari, kuma ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an Kwastam biyu da wani mazaunin Bachaka,” in ji kakakin rundunar, Nafiu Abubakar.

Bayan harin, Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani Bello, ya ziyarci wajen tare da tabbatar wa jama’a cewa hukumomin tsaro na aiki domin kama waɗanda suka kai harin.

“Waɗannan hare-hare na nuni da cewa miyagun suna raguwa saboda yawan farmakin da muke kai musu.

“Za mu ci gaba da yaƙar su har sai mun kawar da su gaba ɗaya,” in ji CP Bello.

Har yanzu, jama’a na cikin fargaba game da tsaro a yankunan kan iyaka, yayin da suke nuna damuwa kan yiwuwar sake kai musu hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Kwastam Lakurawa jami an Kwastam

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce hare-haren da sojojin Amurka ke kaiwa kasar Yemen da keta hurumin yankunanta barazana ce karara ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.

A cikin wata sanarwa da ya fitar yau Juma’a, Baghaei ya yi tir da hare-haren da Amurka ke kai wa Yemen ba bisa ka’ida ba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da raunata jama’ar kasar tare da lalata kayayyakin more rayuwa na kasar.

Ya ce ya kamata kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kawo karshen rashin daukar mataki da kuma yin shiru dangane da farmakin da sojojin Amurka ke kaiwa Yemen.

Ya ce Amurka na ci gaba da kai hare-haren soji kan kasar Yemen tare da kai hari kan kayayyakin more rayuwa na kasar domin daukar fansa kan hadin kan al’ummar Yemen da goyon bayan al’ummar Palastinu da ake zalunta.

Kakakin na Iran ya ce hare-haren na Amurka cin zarafi ne ga ka’idojin Yarjejeniya Ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma ka’idojin dokokin kasa da kasa.

Baghaei ya dorawa gwamnatin Amurka alhakin aikata laifuka.

Kafofin yada labaran kasar Yemen sun ruwaito a safiyar yau Juma’a cewa, an kai wasu sabbin hare-hare a babban birnin kasar Yemen, inda aka kai hari kan wani sansanin soji a kudancin Sana’a da wasu hare-hare guda hudu.

An kuma kai hare-hare a yankunan da ke kusa da filin jirgin sama na Sana’a, baya ga gundumomi biyu a kudanci da tsakiyar lardin Sana’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bayan Hukuncin ‘Yansanda, Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya
  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Wike Ya Jinjina Wa Tinubu kan Bunkasa Ilimi Mai Zurfi
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • ’Yan sanda sun ƙwato wa mutumin da aka sace kuɗin fansarsa a Kano