Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
Published: 27th, March 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na tallafawa shirin inganta ilimi na bunkasa Afirka (BEAR) III, wani shiri na hadin gwiwa da hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) da Jamhuriyar Koriya suka yi.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan wayar da kan jama’a ma’aikatar ilimi ta jihar Kano Balarabe Abdullahi Kiru, yace aikin yana da nufin haɓaka ilimin fasaha da na sana’a a faɗin Afirka, tare da mai da hankali kan ƙarfafa tsarin ilimin fasaha da na sana’a da horo (TVET).
Aikin zai mayar da hankali ne kan harkar noma, tare da mai da hankali kan sarrafa kayan noma da sarrafa su bayan girbi.
A cewar Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda, shirin na BEAR III ya yi daidai da ajandar Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta shirye-shiryen koyon sana’o’i don dogaro da kai.
Ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da hada gwiwa da hukumar UNESCO da kasar Koriya ta Kudu domin bunkasa koyar da sana’o’i a makarantun furamare da na gaba da sakandare a fadin jihar.
Darakta a ma’aikatar ilimi ta tarayya Dr. (Mrs) M.A Olodo ta jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano domin gudanar da taro da masu ruwa da tsaki dangane da aiwatar da shirin na BEAR III.
Ta ba da tabbacin cewa ƙungiyar za ta yi amfani da mafi kyawun lokacin da ya rage don cimma manufofin aikin.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an gina aikin na BEAR III akan ginshikai guda uku: sanya aikin ya dace da bukatun kasashe masu cin gajiyar shirin, da inganta TVET da ake bayarwa, da kuma kyautata fahimtarsa a tsakanin matasa.
Za a gudanar da aikin a kasashe hudu na yammacin Afirka: Najeriya, Ghana, Cote d’Ivoire, da Saliyo.
Rel/ Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome
Yau Asabar Washington da Tehran, ke tattauanwa a birnin Rome na kasar Italiya, wace ita ce ta biyu a shiga tsakanin kasar Oman kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Tattaunwar wacce ba ta gaba-da-gaba ba an gudanar da irin ta a ranar Asabar data gabata a birnin Muscat na kasar Oman, inda bangarorin biyu suka bayyana tattaunawar da mai armashi.
Gabanin tattaunawar ta yau, Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce akwai yuwuwar kulla yarjejeniya da Amurka idan har Washington ba ta gabatar da wasu bukatu na da suka wuce da tunani ba”.
Araghchi ya bayyana hakan ne a yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa da takwaransa na Rasha, Sergei Lavrov, a ranar Juma’a a birnin Moscow, gabanin tattaunawar ta biyu tsakanin Tehran da Washington, da ake shirin gudanarwa yau a birnin Rome na kasar Italiya.
“Za mu tattauna kan batun nukiliya ne kawai, kuma ba za a saka wasu batutuwa a cikin wannan tattaunawar ba,” in ji shi.
Ya kara da cewa “Ina ganin mai yiyuwa ne a cimma matsaya idan [Amurkawa] suka nuna da gaske su ke kuma ba su gabatar da bukatu da ba su dace ba.
Sai dai ya jaddada cewa: “Hanyar diflomasiya a bude take, amma ya nuna matukar shakku game da aniyar Amurka idan aka yi la’akari da matsayin Washington da ke cin karo da juna.
“Muna da matukar shakku game da aniya da manufar bangaren Amurka, amma za mu shiga shawarwarin tare da azama.”Ya kuma jaddada aniyar Tehran ta ci gaba da samar da hanyoyin warware shirinta na nukiliya cikin lumana.