Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-19@17:19:02 GMT

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

Published: 27th, March 2025 GMT

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

An kama mataimakin shugaban ƙasa na farko a Sudan ta Kudu Riek Machar a babban birnin ƙasar Juba, a yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar zaman tankiya tsakaninsa da Shugaba Salva Kiir.

Faɗa tsakanin dakarun da ke goya wa shugabannin biyu baya ya tsananta a yankunan Rejaf da ke kudancin Juba da Wunaliet da ke yammaci.

Rahotanni sun bayyana cewa an kama shi ne tare da uwargidansa Angekina Teny.

Ana samun fargabar cewa kama shi zai iya kawo tarnaƙi ga yarjejeniyar zaman lafiya ta ƙasar.

Kama Machar na zuwa ne bayan shafe makonni ana samun tashe tashe hankula bayan shugaba Kiir ya tsare wasu daga cikin abokan Machar a farkon watan nan.

Tawagar majalisar ɗinkin duniya da ke Sudan ta Kudu tayi gargaɗin cewa ƙasar na cikin barazanar sake faɗawa cikin yaƙi, inda ta buƙaci ɓangarorin biyu suyi aiki da yarjejeniyar zaman lafiya ta 2018.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

Kazalika, Injiniya Xie ya kara da cewa, a cikin rubu’in farko na bana, sashen masana’antu na kasar Sin ya taka rawar gani wajen samun ci gaba ba tare da tangarda ba sakamakon ingantuwar tsari da zurfafa ayyuka wajen samar da sabbin ginshikan bunkasa ci gaba mai inganci. (Abdulrazaq Yahuza Jere).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
  • Babu wanda ya hana Shettima shiga Aso Rock ba— Fadar Shugaban Ƙasa
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Takurawa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima
  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu
  • ‘Yan tawayen Sudan sun kafa tasu gwamnati