HausaTv:
2025-04-19@17:19:00 GMT

Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas

Published: 27th, March 2025 GMT

Bayanai daga falasdinu na cewa an kashe Hamas Abdul-Latif al-Qanou wani kakakin kungiyar Hamas a wani harin da Isra’ila ta kai a arewacin Gaza.

Kamfanin dillancin labaran Quds na Falasdinu ya bayar da rahoton  cewa, jami’in ya yi shahada ne a wani harin da Isra’ila ta kai ta sama a kan tantinsa a garin Jabalia da ke arewacin zirin Gaza.

Har ila yau harin ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da suka hada da kananan yara.

Wannan kisan dai shi ne na baya bayan nan a jerin hare-haren wuce gona da irin da gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza tun a watan Oktoban shekarar 2023, bayan wani dan takaitaccen lokaci inda ta saba ka’idojin tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas, tare da kai munanan hare-hare.

Shahadar al-Qanou ta zo ne kwanaki kadan bayan kisan gillar da gwamnatin sahyoniyawan ta yi wa wasu fitattun jami’an ofishin siyasa na Hamas, wato Ismail Barhoum da Salah al-Bardaweel. An kashe su duka a samame daban-daban.

A baya-bayan nan dai babban mai magana da yawun kungiyar Hamas Sami Abu Zuhri ya jaddada cewa kisan gilla ba zai hana kungiyar ci gaba da fafutukar kwato yankunan Falasdinawa ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato

Shanu 36 sun mutu baya ga wasu 42 da ake zargin an ba su guba guba a kusa da yankin mahaɗar Tafi Gana a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.

Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) a Karamar Hukumar Bassa, Ya’u Idris, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yamma lokacin da shanun ke kiwo a yankin.

Ya’u ya ƙara da cewa an sanya guba ne a cikin gauta, waɗanda aka warwatsa a kewayen wurin kiwon kuma shanun suka ci.

Ya ci gaba da cewa sun kai rahoton lamarin ga dukkan hukumomin tsaro ciki har da Hukumar DSS, da ’yan sanda, ya kuma  Babban Kwamandan Rundunar ta kuma din ya ziyarci wurin da abin ya faru.

Wannan lamarin ya faru ne kwanaki biyu kacal bayan wani mummunan hari a kauyen Zikke, a cikin wannan ƙaramar hukumar ta Bassa, inda aka kashe mutane 52 tare da jikkata wasu da dama. An kuma kona gidaje da dama a harin.

Mazauna yankin da aka kai harin sun zargi makiyaya da hannu a kashe-kashen da aka yi a ranar Litinin, zargin da makiyayan suka musanta.

Kakakin rundunar tsaro ta Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai amsa saƙon da wakilinmu ya aike masa ba game da lamarin a lokacin da ake rubuta wannan rahoto.

An haramta kiwon dare da hawa babur

A sakamakon ƙaruwar rashin tsaro, Gwamna Caleb Mutfwang a ranar Laraba ya haramta kiwon dabbobi da daddare, da kuma jigilar shanu da hawa babura bayan ƙarfe 7 na yamma. Wannan matakin na daga cikin hanyoyin da gwamnatin jihar ta ɗauka domin hana ci gaba da samun sabani tsakanin makiyaya da manoma.

Gwamnan, a cikin wani jawabi da ya yi wa al’ummar jihar a ranar Laraba, ya bayyana cewa a makon da ya gabata, an kai hari kauyen Zikke inda aka kashe mutane da dama.

Sai dai, wannan dokar ta haifar da ce-ce-ku-ce, musamman ma daga direbobin manyan motocin da ke Jos, waɗanda suka bayyana haramcin jigilar shanu bayan karfe 7 na yamma a matsayin wanda ya ci karo da wata doka da ta riga ta hana zirga-zirgar manyan motoci tsakanin karfe 6 na safe zuwa 9 na yamma. Sun kuma roƙi gwamnatin da ta sake duba wannan doka.

Haka kuma, kungiyar MACBAN ta nuna damuwarta game da wannan doka, inda ta bayyana cewa lokacin da aka ƙayyade zai iya shafar rayuwar makiyaya, musamman wadanda za su iya kasancewa tare da shanunsu a kasuwanni bayan karfe 7 na yamma.

Sun cewa suna goyon bayan dokar domin tabbatar da zaman lafiya, amma suna roƙo gwamnan da ya ɗaga lokacin zuwa karfe 8 na dare domin mutanensu su samu damar komawa gida lafiya.

Laifin gwamnatocin baya ne — Gadgi

A nasa ɓangaren, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Pankshin Kanke da Kanam a Jihar Filato, Yusuf Adamu Gagdi, ya bayyana cewa abin takaici ne yadda yankunan da suka yi fice wajen noma a Bokkos, Bassa, Wase, da Mangu suka zama filin daga.

Ya zargi gazawar gwamnatocin baya wajen ba kama shugabannin hukumomin tsaro da laifin  gazawarsu wajen samar da tsaro a yankunansu da ta haifar da karuwar matsalar tsaro a kasar.

Gadgi ya kuma alaƙanta ƙaruwar hare-hare a Filato da tserewar da ’yan bindiga ke yi daga jihohi Zamfara da Sakkwato zuwa dajin Filato sakamakon ragargazarsu da sojoji suka tsananta.

Za mu dawo da zaman lafiya — ’yan sanda

Mataimakin Sufeto Janar na ’Yan Sanda (DIG) Kwazhi Bzigu Dali ya ziyarci yankunan da aka kai hari domin tantance halin da ake ciki, inda ya gudanar da sintiri ta sama da ƙasa tare da ganawa da shugabannin ƙananan hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin da cewa Sufeto-Janar na ’Yan Sanda ya ƙudiri aniyar dawo da zaman lafiya, inda ya sanar da tura karin jami’an tsaro da kayan aiki.

Dattawan Arewa sun fusata

Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kakkausar suka ga kashe-kashen da ake yi a Filato, inda ta bayyana su a matsayin abin kunya ga ƙasa.

Sun soki rashin ɗaukar mataki da Gwamnatin Tarayya ke yi, suna masu kira da a tura jami’an tsaro da kayan aiki nan take tare da tabbatar da an yi adalci.

Haka kuma, Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta nuna baƙin cikinta game da sake ɓarkewar rikicin a Filato, inda ta yi kira ga shugabannin al’umma da na addini da su tallafa wa Gwamna Mutfwang wajen kwantar da hankula da kuma gina zaman lafiya mai ɗorewa.

Gwamnatin Tarayya ta sake nanata ƙudirinta na kawo ƙarshen rashin tsaro a faɗin ƙasar, inda ta bayyana ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsaron kasa.

Tsohon ɗan takarar Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya yi kira ga gwamnatin da ta daina magana ta fatar baki kawai, ta ɗauki matakai na zahiri don kare ’yan Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Gwagwarmayar Yemen Sun Kai Hare-Haren Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Mayakan Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Sun Sake Kunno Kai A Garuruwan Deir ez-Zor Da Hasaka Na Siriya
  • Sheikh Naim Qassem ya yi fatali da kiraye-kirayen kwance amarar kungiyar Hezbollah
  • Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Sake Aiwatar Da Kisan Kiyashi A Sansanin Falasdinawa Na Jabaliya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • Hamas ta gabatar da shawara kan yarjejeniyar musayar fursunoni da tsagaita wuta
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba
  • Hamas ta bukaci hadin kan duniya domin kawo karshen kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza