MDD ta yi gargadi game da tabarbarewar al’amuran jin kai a Gaza
Published: 27th, March 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya ta nuna fargaba kan yadda ake ci gaba da samun karuwar matsalar jin kai a zirin Gaza, inda ta bayar da rahoton cewa akalla Falasdinawa 142,000 ne suka rasa matsugunansu a cikin mako guda kacal saboda tsanantar hare-haren bama-bamai na Isra’ila.
Kakakin MDD Stephane Dujarric, ya bayyana a wani taron manema labarai a jiya Laraba cewa, hare-haren da kuma umarnin gudun hijira, tare da hana kayan da ke shiga Gaza da kuma hana ayyukan jin kai a cikin yankin, suna yin mummunan tasiri ga daukacin al’ummar sama da miliyan biyu.
Dujarric ya yi nuni da cewa, yayin da rikicin ya tsananta, ana sa ran adadin mutanen da suka rasa matsugunansu zai karu sosai.
A yammacin ranar Talata, OCHA ta yi gargadin cewa mutane da yawa a yanzu “suna zaune a kan tituna, suna cikin tsananin bukatar abinci, ruwan sha.”
A ranar Laraba an kashe fiye da mutane 39 tare da jikkata wasu 124 cikin sa’o’i 24 sakamakon hare-haren da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa 40 Ne suka Yi Shahada A Zirin Gaza Sakamakon Ta’addancin Sojojin Mamayar Isra’ila A Jiya Juma’a
Falasdinawa 40 ne suka yi shahada a hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan Zirin Gaza tun daga wayewar garin jiya Juma’a
Rahotonni sun bayyana cewa: A yammacin jiya Juma’a, Falasdinawa fararen hula 8 ne suka yi shahada yayin da wasu kuma suka jikkata sakamakon wani hare-haren da jiragen saman sojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida a sansanin Jabaliya da al-Balad da ke arewacin zirin Gaza.
Haka zalika hare-haren sun yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 6 sannan wasu 8 suka jikkata a wani harin da jiragen saman yakin mamayar Isra’ila suka kai kan taron fararen hula da ke kusa da mahadar Abd al-Aal da ke kan titin al-Jala’a da ke arewacin birnin Gaza.
A cewar majiyoyin cikin gida, jiragen saman yakin mamayar Isra’ila sun kai hari kan wani asibiti da ke titin al-Jala’a, inda suka janyo shahadan Mahmoud Abdullah al-Muqayyad, Ahmed Qaza’ar, Tamer Hamdan, Samer al-Nuwairi, Hatem al-Sa’ati, da Rizq al-Madhoun.
A kudancin zirin Gaza kuwa, Falasdinawa uku ne suka yi shahada, kuma wasu suka jikkata, lokacin da wani jirgin saman yakin mamayar Isra’ila ya kai hari kan wata tanti da ke dauke da ‘yan gudun hijira a yankin Mawasi na Khan Yunis.
Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare a zirin Gaza a rana ta 46 a jere, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar daruruwan mutane, da jikkatan wasu na daban