HausaTv:
2025-03-30@14:28:44 GMT

MDD ta yi gargadi game da tabarbarewar al’amuran jin kai a Gaza

Published: 27th, March 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya ta nuna fargaba kan yadda ake ci gaba da samun karuwar matsalar jin kai a zirin Gaza, inda ta bayar da rahoton cewa akalla Falasdinawa 142,000 ne suka rasa matsugunansu a cikin mako guda kacal saboda tsanantar hare-haren bama-bamai na Isra’ila.

Kakakin MDD Stephane Dujarric, ya bayyana a wani taron manema labarai a jiya Laraba cewa, hare-haren da kuma umarnin gudun hijira, tare da hana kayan da ke shiga Gaza da kuma hana ayyukan jin kai a cikin yankin, suna yin mummunan tasiri ga daukacin al’ummar sama da miliyan biyu.

Dujarric ya yi nuni da cewa, yayin da rikicin ya tsananta, ana sa ran adadin mutanen da suka rasa matsugunansu zai karu sosai.

A yammacin ranar Talata, OCHA ta yi gargadin cewa mutane da yawa a yanzu “suna zaune a kan tituna, suna cikin tsananin bukatar abinci, ruwan sha.”

A ranar Laraba an kashe fiye da mutane 39 tare da jikkata wasu 124 cikin sa’o’i 24 sakamakon hare-haren da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Ayatullah Khatami: Jerin Gwanon Ranar Qudus Rana Ce Mai Matukar Muhimmaci A Musulunci

Wanda ya jagoranci sallar juma’a a nan Tehran a jiya Juma’a ya bayyana cewa; Jerin gwanon ranar Kudus tana da matukar muhimmanci a addinin musulunci, yana mai kara da cewa: Muna godewa Allah madaukakin sarki cewa, ranar kudus ta wannan shekarar ta bunkasa fiye da shekarun baya.”

Haka nan kuma ya kara da cewa; Imam Khumaini ( r.a) da ya ayyana ranar Kudus a duniya a 1979, wacce ita ce juma’ar karshe ta watan Ramadan, a wancan lokacin manyan kasashen duniya masu takama da karfi suna kokarin ganin an mance da batun Falasdinu da kuma kasakantar da shi da cewa batu ne na Larabawa kadai.

Limamin na Tehran ya kuma kara da cewa, abinda Imam Khumain ( r.a) ya yi na ayyana ranar Kudus, wata hikima ce wacce ta dakile makarkashiyar da makiya su ka kitsa.

Ayatullah Khatami ya kuma yi ishara da yadda aka yi jerin gwanon na ranar Kudus a cikin garuruwa da birane 900 a cikin fadin Iran.

A fadin duniya kuwa limamin na Tehran ya yi ishara da cewa an yi jerin gwanon ranar Kudus a cikin kasashe 80 da su ka hada Amurka, Birtaniya, Faransa da kuma Jamus.

Dangane da barazanar da shugaban kasar Amurka yake yi wa Iran, limamin na Tehran ya ce, babu abinda ya iya sai barazana saboda halinsa na tsoro, kuma abin mamaki ne a ce har yanzu bai san cewa, barazanarsa  ba ta da wani tasiri ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Janar Sari: Sojojinmu Sun Yi Taho Mu Gama Da Amurkawa Sau 3 A Cikin Sa’o’i 24
  • ‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
  • Hamas ta yi Tir da kakkausar murya da harin Isra’ila kan masu aikin ceto a Gaza
  • Rikici ya ɓarke bayan wata mata ta mari ɗan sanda a Saudiyya
  • Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  •  Ayatullah Khatami: Jerin Gwanon Ranar Qudus Rana Ce Mai Matukar Muhimmaci A Musulunci
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya