Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa
Published: 27th, March 2025 GMT
Wakilin dindindin na kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Switzerland Chen Xu, ya gabatar da jawabi a jiya Laraba, yayin taro na 58 na kwamiti mai kula da harkokin kare hakkin bil Adama na MDD, don bayyana ra’ayin kasar Sin kan halin da Palasdinu da Isra’ila ke ciki.
A cewarsa, daruruwan fararen hula sun yi asara sakamakon hare-hare ta sama da aka kaiwa zirin Gaza, kuma Sin na matukar adawa da hakan, tare da bayyana bacin ranta game da tabarbarewar matakin tsagaita bude wuta a wurin, wanda aka dauka bayan an sha matukar wahala. Ya ce abin da aka sa gaba cikin gaggawa shi ne kaucewa daukar ko wane irin mataki dake iya tsananta halin da ake ciki, ta yadda za a dakile barkewar bala’in keta hakkin bil Adama da jin kai mafi tsanani.
Chen ya kara da cewa, Sin na adawa da tilasawa fararen hula ficewa daga zirin Gaza. Kana tana goyon bayan shirin farfado da zaman lafiya a Gaza, wanda kasashen Larabawa ciki har da Masar suka gabatar, da farfado da zirin Gaza bisa ka’idar “Barin Palasdinawa su gudanar da harkokinsu da kansu” ba tare da bata lokaci ba.
Har ila yau, Chen ya jaddada cewa, ba za a iya warware batun Palasdinu ba, har sai an koma hanyar da ta dace, wato manufar “Kafa kasar Palasdinu da Isra’ila”. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kasar Guinea Ta Yi Wa Musa Dadis Camara Afuwa
Shugaban gwamnatin soja na kasar Guinea Janar Mamadi Doumbouya ne ya yi wa tsohon shugaban sojan kasar Camara afuwa bayan da aka yanke masa zaman gidan kurkuku bisa laifin kisan kiyashin da ya faru a 2009 a birnin Conakry.
Kafafen watsa labarun kasar ta Guinea ne su ka sanar da afuwar da shugaba Mamadi ya yi wa Camara bisa dalilai na rashin lafiya.
Bugu da kari kakakin fadar shugaban kasa Janar Amara Camara wanda ya yi sanarwar ya ce, an yi hakan ne bisa shawarar da ma’aikatar shari’a ta gabatar.
Camara dai ya mulki kasar ta Guinea ne daga 2008-2009, an kuma yi masa shari’a ne a watan Yuli na 2024, saboda yadda a zamanin mulkin nashi aka yi amfani da karfi wajen murkushe ‘yan hamayya da su ka yi wani taro a cikin filin wasan kwallon kafa.
Fiye da mutane 150 ne dai su ka kwanta dama, kuma jami’an tsaron kasar su ka yi wa mata fiye da 100 fyade.
Shari’ar da aka yi wa Camara wacce ta sami cikakken goyon bayan MDD, ta same shi da lafin gajiyawa wajen hukunta masu laifi.
Matakin na gwamantin yanzu ya biyo bayan shirinta na biyan diyya ga iyalan wadanda aka kashe da kuma yi wa illa.
Sai dai kungiyoyin kare hakkin bil’adama a kasar suna sa alamun tambaya akan wannan matakin na yi wa adalci Karen tsaye.