Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin da ke neman tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
Published: 27th, March 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta janye ƙudurin dokar da ke neman cire rigar kariya ga mataimakin shugaban ƙasa da gwamnoni da mataimakansu.
Hakazalika majalisar ta janye amincewa da ƙudurin da ke neman a soke hukuncin kisa ga masu aikata laifi a ƙasar.
Ƙudurorin biyu na cikin ƙudurori 42 da suka tsallake karatu na biyu a jiya Laraba.
Shugaban masu rinjaye na majalisar Julius Ihonvbere ne ya gabatar da ƙudurin janyewar.
Mataimakin kakakin majalisar Benjamin Kalu ya ce an ɗauki matakin janyewar ne domin bayar da damar yin muhawara kan ƙudurorin bayan cece-kucen da hakan ya haifar a faɗin ƙasar.
Ƙudurorin na daga cikin gwamman ƙudurorin da majalisar ke nazari a kansu, a wani ɓangare na yin gyaran fuska ga kundin tsarin mulkin ƙasar na shekarar 1999.
Aminiya ta ruwaito cewa, majalisar ta janye ƙudirin ne bayan gwamnatocin jihohin sun bayyana adawarsu kan matakin da ke neman tuɓe musu rigar alfarmar da ke bai wa gwamnoni da mataimakansu da kuma mataimakin shugaban ƙasa kariya daga fuskantar tuhuma kan laifuka.
A ranar Larabar da ta gabata ce ƙudirin ya samu karatu na biyu a zauren majalisar, ƙarkashin jagorancin mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
Hukumomi a Myanmar sun ce adadin wadanda suka mutu a girgizar kasar ya kai 1,644, yayin da wasu 3,408 suka jikkata, ye zuwa ranar Asabar din nan.
Tunda farko dai mutane 1,007 ne aka sanar sun mutu sai wasu 2,389 da suka jikkata.
Girgizar mai karfi maki 7.7 ta shafi Kasashen Myanmar da Thailand wadanda suk suka ayyana dokar ta baci a ranar Juma’a.
Tuni kasar Myanmar ta nemi taimakon kasashen duniya da kuma kungiyoyi don agazawa wadanda girgizar kasarta shafa.
Kasar Iran ta ce a shirye take ta taimakawa kasashen biyu da girgizar kasar ta shafa.
A wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya fitar yau Asabar ya ce Iran a shirye take ta shiga ayyukan agaji da ceto a kasashen biyu.
Baghai ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa da kuma gwamnatoci da al’ummomin kasashen biyu.
Ayyukan agaji na kasa da kasa sun fara kwararowa cikin kasar: masu aikin ceto da agaji da suka hada da barguna, kayan abinci da na bincike, daga kasashen China da Indiya da ke makwabtaka da su, da kuma wasu kasashe.