Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya
Published: 28th, March 2025 GMT
Masu fashin baki da dama na da ra’ayin cewa, tabbas illar wannan mataki na Amurka zai koma kanta, inda wasu daga sassan raya tattalin arzikin kasar kamar na albarkatun gona, da makamashi za su iya fuskantar matsin lamba mai tsanani. Yayin da wasu sassan kamfanonin kasar kuma ka iya fuskantar raguwar ribar da suke samu da kaso mai yawa, sakamakon karin kudaden hajojin da ake samarwa a masana’antun kasashen da Amurkan ta karawa haraji.
La’akari da wadannan illoli, kamata ya yi Amurka ta yi karatun ta nutsu, ta dakatar da matakan kakaba haraji marasa ma’ana, kana ta koma teburin tattaunawa, domin warware duk wani sabani na kasuwanci da cinikayya tare da dukkanin sassan da batun ya shafa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya ce hare-haren da sojojin Amurka ke kaiwa kasar Yemen da keta hurumin yankunanta barazana ce karara ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.
A cikin wata sanarwa da ya fitar yau Juma’a, Baghaei ya yi tir da hare-haren da Amurka ke kai wa Yemen ba bisa ka’ida ba, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da raunata jama’ar kasar tare da lalata kayayyakin more rayuwa na kasar.
Ya ce ya kamata kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kawo karshen rashin daukar mataki da kuma yin shiru dangane da farmakin da sojojin Amurka ke kaiwa Yemen.
Ya ce Amurka na ci gaba da kai hare-haren soji kan kasar Yemen tare da kai hari kan kayayyakin more rayuwa na kasar domin daukar fansa kan hadin kan al’ummar Yemen da goyon bayan al’ummar Palastinu da ake zalunta.
Kakakin na Iran ya ce hare-haren na Amurka cin zarafi ne ga ka’idojin Yarjejeniya Ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma ka’idojin dokokin kasa da kasa.
Baghaei ya dorawa gwamnatin Amurka alhakin aikata laifuka.
Kafofin yada labaran kasar Yemen sun ruwaito a safiyar yau Juma’a cewa, an kai wasu sabbin hare-hare a babban birnin kasar Yemen, inda aka kai hari kan wani sansanin soji a kudancin Sana’a da wasu hare-hare guda hudu.
An kuma kai hare-hare a yankunan da ke kusa da filin jirgin sama na Sana’a, baya ga gundumomi biyu a kudanci da tsakiyar lardin Sana’a.