Mai magana da yawun ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya bayyana cewa, kasar tana matukar adawa da yunkurin Amurka na kara yawan dozin-dozin na kamfanoninta a cikin jerin kamfanonin da aka takaita fitar da kayayyakinsu zuwa kasashen waje.

Jami’in, wanda ya bayyana haka a ranar Larabar nan, ya ce, matakin na Amurka ba komai ba ne illa murkushewa da kuma takura wa wasu kamfanonin kasashen ketare, tare da danne hakkokin sauran kasashen duniya na samun ci gaba.

Yana mai cewa, hakan zai yi matukar cutar da kamfanonin tare da kawo cikas ga kwanciyar hankali da samun wadataccen tsarin samar da kayayyaki a duniya.

Ya kara da cewa, matakin zai yi kafar ungulu ga kokarin warware matsaloli ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa, kuma kasar Sin tana kira ga Amurka da ta gaggauta kawo karshen kurakuran da take tafkawa, kana ya ce, kasar za ta dauki matakan da suka dace don kiyaye hakkoki da muradun kamfanonin Sinawa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban CMG Ya Gana Da Ministar Raya Al’adu Ta Rasha

Yau Juma’a, shugaban babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin CMG Shen Haixiong, ya gana da ministar raya al’adu ta kasar Rasha Olga Lyubimova dake ziyara a kasar Sin.

Shen Haixiong ya ce, yana maraba da Rasha ta shiga a dama da ita cikin bikin fina-finai na kasa da kasa da 0za a yi a kasar Sin a bana.

A nata bangare, Olga Lyubimova ta ce, a shekarun baya bayan nan, Rasha da Sin suna kara musaya a fannoni daban-daban, ciki har da fina-finai, kuma sun samu kyawawan sakamako. Ta kara da cewa, tana fatan bangarorin biyu za su zurfafa hadin gwiwarsu. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • Kamfanonin Kasashen Waje Na Da Imani Kan Ingancin Kasuwar Kasar Sin 
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  •  Ayatullah Khatami: Jerin Gwanon Ranar Qudus Rana Ce Mai Matukar Muhimmaci A Musulunci
  • Shugaban CMG Ya Gana Da Ministar Raya Al’adu Ta Rasha
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • Jerin Gwanon Ranar Kudus Na Ci Gaba Da Gudana A Kasashen Duniya