Gwamnatin Amurka Tana Shirin Dakatar Da Bada Kudaden Tallafi Don Samar Da Wasu Magunguna
Published: 28th, March 2025 GMT
Gwamnatin kasar Amurka tana shirin dakatar da bada kudade ga hukumar GAVI wacce take samar da alluran riga kafi don tallafawa kasashe masu tasowa daga ciki har da tarayyar Najeriya.
Jaridar Daily Trus ta Najeriya ta nakalto wata sanarwa daga hukumar USAID bayar inda take cewa gwamnatin shugaba Donal Trump yana son janye tallafin da kasarsa ke bayarwa don wannan shirin, wanda yake yakar cutar Malaria da wasu cututtuka a wadannan kasashe.
Labarin ya kara da cewa za’a dakatar da ayyukan samar da magunguna da alluran riga kafa har guda 5,341 idan an dakatar da tallafi, wanda yake cinye dalar Amurka biliyon 75 a ko wace shekara. A halin yanzu dai hukumar ta USAID ta bada dalar Amurla biliyon 48, don samar da wasu magungunan da alluran riga kafi n awannan shekarar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
Ndume, ya yaba wa jarumtakar dakarun Nijeriya, amma ya buƙaci ƙarin matakan tsaro.
Ya buƙaci gwamnati ta taimaka wa ƙungiyoyin tsaron al’umma da kayan aiki da makamai na zamani.
Wannan harin na daga cikin jerin hare-haren da ake fama da su a Jihar Borno a cikin ‘yan kwanakin nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp