Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa gwamnatin kasar ta Mayarwa Shugaban kasar Amurka Donal Trump amsar wasikarsa ga kasar danagne da shirinta na makashain Nulkiya ta hanyar kasar Omman.

Aragchi ya bayyana haka a jiya Alhamis a lokacinda yake hira da kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran.

Ya kuma kara da cewa a cikin wasikar dai gwamnatin JMI bayyanawa shugaban kan cewa tana ganin bazata iya shiga tattaunawa gaba da gaba da Jami’an gwamnatin kasar Amurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya ba, saboda halayen gwamnatocin Amurka a baya dangane da shirin.

Daga ciki Iran ta dauke shekaru biyu cutar tana tattauna batun wannan shirin da manya-manyan kasashen duniya daga ciki har da kasar Amurka,  aka cimma yarjeniya a shekara ta 2015, kuma har an fara aiwatar da yarjeniyar ta JCPOA, amma gwamnatin Amurka ta lokacinda wanda shugaba mai ci yake jagoranta ta fice daga cikin yarjeniyar ba tare da wani dalili ba, sannan ta dorawa Iran sabbin takunkuman tattalin arziki mafi muni a tarihin kasar da nufin tilasta mata da sake wata tattaunawa  da ita. Waya ya sani mai yuwa da sake saba alkawalin da aka cimma da ita a wannan karon ma, bayan wancan?. Amma ta kasa samun nasara har ta sauka.

Banda haka a lokacinda wannan gwamnatin ta zo kan karagar shugabancin Amurka ta fara kara dorawa JMI wasu karin takunkuman tattalin arziki kafin ma ta gayyana kasar zuwa tattaunawa.

Wannan ya nuna cewa ba tattaunawa take bukata ba, sai dai tursasawa. Wanda kasar Iran baza ta taba amincewa da haka ba.

Sannan idan Amurka ta na son shiga tattaunawa da Iran kan shirinta na makamashin Nukliya to a halin yanzu ma tana tattaunawa da kasashen turai uku kan shirin nata. Sai ta shigo.

 

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah

Ofishin jakadancin Amurka da ke Damascus ya fitar da wata sanarwar gaggawa, inda ya yi kira ga daukacin Amurkawa da su gaggauta ficewa daga kasar Syria, sakamakon karuwar hare-haren da ake kai wa a lokacin bukukuwan sallar Idi, wanda ke kawo karshen azumin watan Ramadan mai alfarma.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta daukaka tafiye-tafiye zuwa Syria zuwa mataki na 4 mafi girman inda aka gargadi, Amurkawa da kada su je kasar Siriya bisa kowane dalili.

Ofishin jakadancin ya gargadi ‘yan kasar game da yiwuwar kai hari kan “ofisoshin jakadanci, kungiyoyin kasa da kasa da cibiyoyin jama’a na Syria” a Damascus.

Halin tsaro a Syria ya tabarbare bayan da kungiyoyin ‘yan ta’adda, karkashin jagorancin Hay’at Tahrir al-Sham, suka hambarar da gwamnatin Bashar al-Assad a ranar 8 ga Disamba, 2024.

Tun bayan rugujewar gwamnatin Assad, sojojin Isra’ila ke kai hare-hare ta sama a kan cibiyoyin soji, da kuma rumbun adana kayan yaki na sojojin Siriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Pezeshkian: Iran Ba Za Ta Yi Tattaunawa Kai Tsaye Da Amurka Ba
  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
  • Kwamandan IRGC Ya Gargadi Amurka Dangane Da Hari Kan Kasar A Ranar Qudus Ta Duniya
  • Gwamnatin Amurka Tana Shirin Dakatar Da Bada Kudaden Tallafi Don Samar Da Wasu Magunguna