A yayin da watan Ramadan ɗin wannan shekara yake bankwana, ga abubuwan da malamai suka bayyana game da fitar da Zakkar kono, wato Zakatul Fidr ga duk wanda ke da hali.
Sahabi Abdullahi Ibn Abbas ya ruwaito cewa: “Manzon Allah (SAW) wajbata fitar Zakkar kono domin kankare kurakurai da yasassun maganganun da mai azumi ya yi, sannan sadaka ce ga miskinai.
Daga cikin hikimar bayar da ita, akwai sanya wa miskinai farin ciki ta hanyar samar musu da abin da za su ci a lokacin Ƙaramar Sallah.
Yadda ake fitarwaMutum zai fitar wa kansa da kuma waɗanda yake ciyarwa kamar mata, ’ya’ya da ma’aikata da sauransu idan Musulmai ne.
“Manzon Allah Ya wajabta fitar da zakkar kono ga babba da yaro, ’yantacce da bawa, daga cikin wadanda kuke ciyarwa,” kamar yadda Abdullahi bn Umar ya ruwaito a Hadisi.
Mai fitar da zakkar zai fara ne da fitar wa kansa, sannan sauran mutanen gwargwadon wajibcin ciyar da su a kansa.
Adadin da ake fitarwaKowanne mutum ɗaya za a fitar masa da Sa’i ɗaya, wato Mudun Nabi hudu.
Idan babu Sa’i ko Mudun Nabin awo, ana iya aunawa da tafin hannu.
Malamai sun ce Mudun Nabi ɗaya daidai yake da cikin tafin hannu biyu na matsakaicin mutum.
Abin da ake fitarwaAna fitar da zakkar kono ce daga nau’in ɗanyen abincin mutanen garin.
Ana fitarwa ne daga abin da ya ƙaru a kan abincin rana da yinin mai fitarwa da iyalansa a lokacin.
Lokacin fitarwaMalamai sun bayyana cewa ya halatta a fitar da zakkar tun daga ranar 28 ga Ramadan.
Hadisi ya nuna, “Abauullahi bn Abbas kan ba da ita da kwana ɗaya ko kwana biyu kafin ranar Sallah.”
Amma tana wajaba ne daga safiyar ranar Ƙaramar Sallah, a kuma gama kafin Sallar Idi.
“Wanda ya bayar kafin sallah to zakka ce karɓaɓɓiya, wanda ya bayar bayan sallah kuma to sadaka ya bayar kamar sauran sadakoki.”
Malamai sun ce haramun ne a jinkirta fitar da da ita ba tare da uzuri ba.
Waɗanda ake bai waHadisi ya nuna miskinai ake bai wa.
Wasu malamai na ganin ana iya ba da ita ga sauran mutanen da ake ba wa zakkar farilla (bayi, matafiya, masu bashi a kansu, masu aikin karbar zakka, masu aikin fisabilillahi, wadanda ake kwadayin su musuluntar).
Wanda aka ba wa zakkar shi ma zai fitar, idan har an samu ragowa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ciyarwa Zakkar Kono fitar da zakkar kono a fitar da zakkar
এছাড়াও পড়ুন:
GORON JUMA’A
Ina gaida Ummi da Baba sai ‘yan uwana yaya Zahra, Yaya Aminu, Yaya Hadiza, Yaya Maimuna, Yaya Rashida, Iman, Amir Da Nurain, sannan kawayena Badi’a Kabir Kwallo, Jamila Sa’ad, Zainab Garba Goro, Yahanasu Imam, Saddika Junaid, Hauwa Uwaisu, da fatan sun yi Juma’a lafiya.
Sako Daga Fatima Zahra Jihar Kano:
Ina gaida Mamana da Abbana da kawaina kamar Rafi’a Kamal, Walida Sadik, Maryam Aliyu, Amina Idris, Khadija Baba, A’isha Fahat, Kursiyya Hamisu, Fiddausi da dai sauransu.
Sako Daga Wasila Adam Nuhu Jihar Kaduna:
Ina gaida Anti A’isha, Anti Ladidi, Anti Balaraba, Uncle Zubair, Uncle Jafar, Uncle Kamalu, Uncle Tajuddeen, Anti Kubra, Anti Sadiya, Uncle Yakub, sai kawayena kamar su; Shaheedah, Yasmin, Zeenat, Meenah, Mahmah, Hanan, Afnan, Fauzy, Ruky, Rumaisa.
Sako Daga Maryam Murtala, Jihar Kano:
Ina gaida Mamy, Maryam Abdullahi, ina gaida kawayena kamar, Khurthum Nasir, Zainab A. Mudi, Halima Saleh, Fatima Kabir Kanwa, Asma’u Muhammad Bello, Muhammad Abdullahi Aminu Mudi, Anwar, Baby Maryam, Anti Fauziyya, Bulun-bulun, Anti Sidiya, Ameerah, Amina, Esha, Anti Safiyya, Mama, Khairiyya, Uncle Hassan, Ibrahim, Uncle Aminu da fatan za su yi juma’a lafiya.
Sako Daga Maryam’s Bakery:
Ina gaida Mum da Dad nawa sannan ina gaida Sisters da brothers dina sai students dina irin su; Deejah, Meerah, Yusra, Nahnah, Zee, Fati, Husna, Priciliar, Kueen Billy, Zainab (first lady), princess Mahmah, Glory, Faith, Maryam Sha’aban, da dai sauran su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp