Leadership News Hausa:
2025-04-20@12:12:59 GMT

Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi

Published: 28th, March 2025 GMT

Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi

Yadda Ake Ba Da Ita

Ana ba da ita kafin a fita zuwa Sallar Idi ko kafin Ranar Sallah da kwana daya ko biyu. Abin da ake bayarwa shi ne Muddan Nabiyy (mudun awo ne dan madaidaici wanda za a iya auna shi da cikin tafukan hannun mutum mai matsakaicin tsawo) guda hudu a kan kowane mutum. Ana fitarwa daga dukkan nau’in abinci, kamar mu a nan mu ce shinkafa, masara, doya, dawa, dauro, cukwi, nono da duk dai abin da galibin mutane suke amfani da shi a matsayin abinci.

Malaman kasar Maroko wadda kasa ce ta Malaman Musulunci kuma ‘yan’uwanmu ne Malikawa; sun yi fatawa cewa ya halasta a ba da kudi a madadin abinci a Zakkar. Za a kimanta kudin adadin Muddan Nabiyy hudu da za a fitar sai a ba da. Wannan ya halasta.

Idan mutum ya yi nazarin hikimar ba da Zakkar, wato wadata talakawa da miskinai don kar a gan su suna bara saboda rashin abincin da za su ci a Ranar Sallah, wannan kudin da za a ba su sai ya fi musu dadi a kan tsabar abincin. Domin wani idan ka bashi hatsin watakila ba zai iya nikowa ba, toh ka ga shi a wurinsa kudin zai fi masa amfani fiye da dawa ko masara. dan dama-dama shinkafa ko doya wanda duk za a iya dafawa ba sai an nika ba. Amma fa a lura, kowane irin abinci mutum ya bayar ya yi. Saboda amfanin kudin ne ya sa muka kawo wadannan bayanan.

An fi so a ba da Zakkar ga mutanen kirki daga cikin talakawa ko wadanda suke da almajirai a hannunsu wadanda idan an ba su ba za su je bara ba a ranar. Ita Shari’a ba ta so a ga kaskancin mutum a wannan ranar, so ake kowa ya nuna girman Musulunci, kodayake wasu ‘yan’uwa ba za su yarda ba, duk abin da aka ba su ba za su iya hakura ba sai sun fita bara. Toh amma kuma kar wannan ya sa a ce ba za a ba su ba.

Idan mutum ya fitar da Zakkar sai ya kasance babu miskinai a kusa da shi da zai ba su, to ya dauka ya kai wurin da suke ya ba su, kar ya ce ai tunda babu miskinai a kusa da shi shikenan ba sai ya ba da ba.

Fa’ida: hatta kafirin da ake zaune da shi in talaka ne za a iya ba shi Zakkar don ya wadata a wannan ranar. So ake dan Adam ya zama ya wadata saboda albarkar ranar ta Sallah.

Sallar Idi

Sallar Idin Shan Ruwa (karamar Sallah) da Sallar Idin Layya (Babbar Sallah kamar yadda galibin Hausawa ke cewa), an shar’anta su a Musulunci a shekarar farko da yin Hijirar Annabi (SAW) daga Makka zuwa Madina. Kuma Annabi (SAW) ya dauwama a kansu (yana aikatawa). Ya hori maza da mata da yara da manya su fita zuwa gare su, ma’ana su je Masallacin Idi.

Ana so a yi wanka, a sa turare, a sanya mafi kyan tufafi da mutum yake da shi. A Sallar Idin Shan Ruwa, ana so a ci abinci kafin a fita zuwa Masallaci koda dabino ne ko shayi. Ana so a dan jinkirta ta kadan; savanin Sallar Idin Layya da aka fi so a jinkirta cin abinci har sai an dawo. Idan mutum ya samu ikon yin Layya; ana so ya bude baki da naman Layyar sannan an fi so a gaggauta yin ta domin a dawo gida a yi Layya.

Ba a yin Sallar Idi (duka biyun) a Rufaffen Masallaci sai dai in akwai lalura kamar ta ruwan sama. A wajen gari ake fita yin SallarIdodin biyu ko kuma duk filin da aka samu. Annabi (SAW) bai tava yin Sallar Idi a Rufaffen Masallaci ba sai sau daya saboda ruwan sama kamar yadda Hakim ya ruwaito Hadisin.

Ana so a canja hanyar da aka je Masallacin Idi wajen dawowa amma ba dole ba ne. Ana so a yi Sallar Idin Shan Ruwa kamar da misalin karfe bakwai da rabi na safe (7:30am), Sallar Layya kuma kamar da misalin karfe bakwai na safe (7:00am). Amma ko sun kai karfe goma sha daya na rana babu laifi, duk lokacin yin su ne.

Ba a yin Kiran Sallah ko Ikamah ko cewa “a tashi a yi sallah”. Da zarar Sarki ko wanda ya tsaya a matsayinsa ya iso filin masallaci sai a mike a shiga Sallah. A raka’ar farko; bayan Kabbarar Harama sai a kara Kabbara shida, sun zama bakwai kenan. A raka’a ta biyu; bayan Kabbarar Tasowa daga Sujuda sai a kara Kabbara biyar, sun zama shida kenan. Ba a yin Nafila kafin Sallar Idi (duka biyu) kuma ba a yi a bayanta. Liman zai yi huduba bayan an yi sallama, wanda yake so zai zauna ya ji wanda wani uzuri ya kama shi sai ya tashi ya tafi ba tare da ya yi magana (surutai) ba.

Ana so a yi wasanni, da kade-kade, da wake-wake, da ciye-ciye, da nishadi, da ziyarori, da yi wa juna murnar Idi. Ana so a yi kallon wasannin ko rawar da ake yi, duk ya halatta a wannan ranar. Wannan shi ne Musulunci sassauka kamar yadda Annabi (SAW) ya fada, Tirmizhi da Ibn Majah da Baihaki suka fitar.

Allah ya sa mu kammala Azumi lafiya, mu yi Sallah lafiya, ya hore wa dukkan Musulmi abin da za a yi hidimomin Sallah da shi, Allah ya karva mana ibadunmu kuma ya karve mu da falalarsa albarkar Annabi (SAW).

 

‎Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadi wa ala alihi hakka kadrihi wa mikdarihil aziym.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Dausayin Musulunci Sallar Idin

এছাড়াও পড়ুন:

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

Masu wannan fahimta sun yi imanin cewa duk lokacin da mutum ya ji baya son wani abu to a wurinshi wannan abin ba mai kyau ba ne. Haka nan kuma duk lokacin da mutum ya ji cewa ga wani abu amma shi ne ya kwanta mashi, toh wannan abin shi ne mai kyau.

Babban misalin da wadannan masu ra’ayi suke jaddadawa da nanatawa a kullum shi ne cewa a lokacin da mutum ya yi tsammanin cewa wani abu na da kyau a ra’ayinshi, to idan ya je cikin wata al’ummar zai tarar da cewa wannan abin barna ko wani abin ki. Misali da shan giya, caca da sauransu.

Da irin wannan nazari ne aka samar da mafi shaharan nazariyyar nan ta NIHILISM, wanda ya zo da wasu ‘yan sauye-suye. Fahimtar ta Nihilism ta ce, sam babu wata doka da za ta iya bambancewa tsakanin abu mai kyau da mara kyau. Don haka ta hanyar ra’ayi da mahangar mutum ne kawai zai iya bambancewa tsakanin mai kyau da marar kyau.

Masu fahimta irin ta Nihilism sun tafi a kan cewa, dabi’ar mutum da yanayin mu’amalarsa da mutane ne kadai za ta iya ayyana nagartacciyar rayuwa ya ke yi ko akasinta. sannan kuma zantukan yabo ko zagi daga makusantan mutum su ma za su iya fayyace irin rayuwar da ya ke yi, ma’ana, abubuwan da suke fadi a kan shi.

Kowanne mutum yana dauke da wasu nauyayen abubuwa na irin dabi’un da ya kamata ya nunawa makusantanshi. Misali da akwai hakkoki na dabi’a da su ka wajaba akan shi wadanda da su ne zai mu’amalanci iyayensa. Haka nan shugaba akwai dabi’o’in da su ya kamata ya mu’amalanci mutanen da ya ke shugabanta.

Bayan samuwar wannan fanni na Nihilism, wanda shi ma ya zo da gudummawarsa dangane da yadda mutum zai gabatar da nagartacciyar rayuwa, sai masanin falsafa Plato ya bulla da sabon nazari wanda kaitsaye ya ke kalubalantar tushen nazariyyar Nihilism din. nazarin na shi ne ya yi kaurin suna har a ke yi masa lakabi da PLATONISM.

Plato cewa ya yi bayani kan wata babbar hanya da mutum zai bi ya gudanar da nagartacciyar rayuwa, inda a takaice ya ce, ‘Mutum ya nemi ilmi’. Ya ci gaba da cewa, a dai dai lokacin da mutum ya samu ilmi ya fahimci me ake nufi da nagartacciyar rayuwa, lallai babu wani abu da zai hana shi bin wannan hanya.

Plato ya ce aikata alfasha da masha’a duk suna aukuwa ne saboda karancin ilmin mai aikata su. Idan mutum ya fahimci ga gaskiya, ita zai bi domin gudanar da nagartacciyar rayuwa.

An zargi wannan nazarin da cewa, ta ya ya mutanen da ke da mabanbantan fahimta za su iya yin ilmin da za su yi nagartacciyar rayuwa? Sai ya ci gaba da bayanin cewa mutum duk ilminsa ba zai iya gano yadda ya kamata ya yi rayuwa ta gari ba, har sai ya samu horo na musamman dangane da abin da ake nufi da abu mai kyau da mara kyau.

Mutumin kuma da bai da kwakwalwar da za ta iya fahimtar karatu sai ya rika koyi da wadanda su ke da ilmi da horon gudanar da rayuwa mai kyau.

Plato ya ce, lura da tarbiyyar yara tana da muhimmanci wurin basu horo da ilmi, wanda kuma hakan zai sa su samu halayen kwarai da dattako. Yana da kyau al’umma ta yi kokarin ganin cewa wadanda ke mulkarsu (shugabanni) mutane ne masana, masu halin dattako da natsuwa da zurfin ilmi.

Lokacin da nazariyyar Platonism ta bayyana ta zama tamkar kishiya ga Nihilism. Domin kai tsaye nazarin ya yi dirar mikiya ne akan Nihilism da ra’ayoyinsa. kuma wannan tunani na Platonism ya samu karbuwa dari bisa dari a falsafar addinai. Sai dai wasu ‘yan bambance-bambance da ba za a rasa ba, da kuma gyare-gyare.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 8 Kan Zargin Kashe Jariri A Borno
  • Yadda Za Ku Hada ‘Mimi Fankek’
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (2)
  • Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare
  • Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP
  • Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
  • Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle