Aminiya:
2025-04-20@11:53:54 GMT

Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m

Published: 28th, March 2025 GMT

Mai Bai Wa Gwamnan Sakkwato Shawara kan Harkokin Karkara, Malami Muhammad Galadanchi (Bajare), ya bai wa magoya bayan jam’iyyar APC a jihar, kyautar Naira miliyan 22 domin gudanar da shagalin Sallah Karamar.

Yayin bayar da kyautar a ranar Alhamis, Bajare ya ce ya yi hakan ne domin nuna godiyarsa ga jagoran APC a jihar, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, da Gwamna Ahmad Aliyu, bisa damar da suka ba shi don ba da gudunmawarsa ga ci gaban jihar.

An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Isuhu Yellow a Zamfara Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu

“Wannan tallafi saƙon godiya ne daga shugabanninmu zuwa gare ku. Idan ba su ba mu dama ba, ba za mu iya wannan ba.

“Kuma muna shirye mu ƙara tallafawa a duk lokacin da buƙata hakan ta taso,” in ji shi.

Ya jinjina wa al’ummar Ƙaramar Hukumar Sakkwato ta Arewa, bisa sadaukarwar da suka yi wajen ganin jam’iyyar APC ta yi nasara, inda ya ce hakan ne ya sa suka cancantar a yi masu hidima.

Bajare, ya tabbatar da cewa zai ci gaba da tallafa wa magoya bayan jam’iyyar lokaci zuwa lokaci domin tabbatar da ci gaban tafiyar siyasarsu.

Dangane da tsarin rabon tallafin, ya ce kowane mutum da aka zaɓa zai amfana da kuɗi tsakanin Naira 100,000 zuwa miliyan ɗaya, ya danganta da matsayinsa.

Haka kuma ya yi fatan al’umma za su gudanar da shagalin sallah cikin lumana da kwanciyar hankali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kyautar Kuɗi Magoya Baya Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Rurum Ya Shawarci Mafarautan Arewa Da Su Daina Zuwa Kudu Farauta 

Ya bayyana cewa shiga wani yanki da ba a fahimtar yaren juna ɗauke da makamai na iya janyo fargaba da tashin hankali.

“Ka yi tunanin idan wasu daga Kudu sun shigo ƙauyanku ɗauke da makamai kuma ba ku fahimtar yaren juna — za ku ji tsoro. Haka nan idan mutanenmu suka shiga yankin Kudu da makamai, su ma za a ji tsoro,” in ji shi.

Rurum ya ce zai gana da shugabannin ƙungiyoyin masu farauta a jihar domin daƙile wannan ɗabi’a, ya kuma buƙace su da su nemo hanyar nema wa kansu asiri .

“Wasu su tafi farauta su dawo ba tare da sun kamo ko ɓeran daji ba. Bai dace su ci gaba da haka ba. Ya kamata mu nemi wata hanya ta zaman lafiya da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Haka kuma, ya bayar da gudunmawar naira miliyan biyar ga iyalan waɗanda suka rasu, sannan ya sha alwashin gina makaranta a garin domin girmama su.

Rurum ya kuma ce zai haɗa kai da Sanata Kawu Sumaila domin su kai ƙudiri a majalisa a kan kisan da aka yi wa mafarautan jihar a garin Uromi don ganin an yi wa waɗanda abin ya shafa adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
  • Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
  • Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Bukaci Kiristoci Da Su Tuna Da Darussan Lokacin Ista
  • Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
  • Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Rurum Ya Shawarci Mafarautan Arewa Da Su Daina Zuwa Kudu Farauta