WFP: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Karanci Abinci A Nijeriya
Published: 28th, March 2025 GMT
Wani sabon rahoto da hukumar samar da abinci ta duniya (WFP) ta fitar a Nijeriya, na ishara da cewa mutum miliyan 11 ne a fadin jihohi shida na Arewa maso Gabas da Arewa maso Yammacin Nijeriya ke fuskantar matsalar karancin abinci a shekarar 2025.
Kazalika, rahoton ya danganta matsalar da rashin tsaro da ake ci gaba da fuskanta, da hauhawar farashin kayan abinci da man fetur, da bala’in yanayi, da kuma matsugunan jama’a, ya sa miliyoyin mutane ke fafutukar samun abinci mai gina jiki.
Rahoton UNICEF ya kara bayyana cewa yara ‘yan kasa da shekaru biyar a Nijeriya, kusan miliyan 11, na fama da matsanancin rashin abinci, wanda hakan ya sa kashi 50 cikin 100 na ka fuskantar barazana ga rayuwarsu.
Rahoton ya bayyana rashin wadataccen abinci mai gina jiki, da wahalhalun tattalin arziki na iya zama ummul-haba’isin muhimman abubuwan da ke haifar da rashin abinci ga yara.
A cikin 2024 kadai, kungiyar (MSF) ta ce ta yi wa yara sama da 300,000 maganin tamowa, doriyar kashi 25 cikin 100 daga 2023.
Daga cikin wadannan kaso, 75,000 na bukatar kulawar rashin lafiya mai tsanani, yayin da 250,000 aka basu kulawa ta hanyar shirye-shiryen sama musu lafiya a fadin jihohi bakwai: Borno, Bauchi, Katsina, Kano, Sokoto, Zamfara, da Kebbi.
Wakilin kungiyar ta MSF na kasa Dr Simba Tirima ya shaida wa LEADERSHIP cewa kungiyar agajin ta lura da yadda ake samun karuwar masu dauke da cutar, wanda ya zarce shekarun baya a duk cibiyoyin kula da lafiyarsu.
“Rashin abinci mai gina jiki na kara ta’azzara, tare da samun karin yara a wuraren da ake kula da su,” in ji Dr Tirima.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Minista Ya Sake Jaddada Ƙudirin Sabunta Kayan Aikin Watsa Labarai Na Gwamnati
Waɗanda suka take wa Ministan sawu a tafiyar su ne jagororin hukumomin yaɗa labarai da wayar da kai da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa.
Ya yi zama daban-daban tare da ƙwararru inda suka tattauna kan yadda za a inganta ƙwarewa da kuma kayan aiki na zamani na kafafen yaɗa labarai na gwamnatin Nijeriya.
Ya ce: “Ina sanar da ku waɗannan abubuwan ne domin jaddada ƙudirin gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu cigaba mai ɗorewa a fannin watsa labarai a ƙasar nan.
“Wannan ne ma ya sanya muke gudanar da irin wannan taron bita na ministoci, da kuma shirin ƙaddamar da Taron Tattaunawa da Jama’a a sassan ƙasar nan nan gaba kaɗan.”
Idris ya kuma bayyana halartar da ya yi a Taron Kasuwanci na Nijeriya da aka yi a birnin Paris, ƙasar Faransa, wanda kamfanin Business France ya shirya.
A gefen taron, Idris ya gana da manyan jami’an hukumar UNESCO domin ƙara inganta shirin kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai a birnin Abuja.
A cewar sa, wannan cibiyar za ta taimaka gaya wajen bunƙasa hazaƙar ‘yan jarida da kuma gina sahihin tsarin yaɗa labarai mai inganci a ƙasar nan.
Ya ce: “Cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wurin ƙara ƙarfin gwiwa da ingancin aikin ‘yan jarida a Nijeriya.”
Idris ya ƙara da cewa shirye-shiryen da ake yi kamar wannan taron bita da kuma Taron Tattaunawa da Jama’a da ke tafe, yana daga cikin dabarun gwamnatin don ƙarfafa gaskiya, ƙarfafa tattaunawa tsakanin gwamnati da al’umma, da kuma ƙarfafa amincewa a tsakanin ɓangarorin biyu.
A yayin taron, Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka don gyara ɓangaren wutar lantarki domin tallafa wa shirin gwamnati na bunƙasa masana’antu da tabbatar da isasshiyar wutar lantarki ga ‘yan Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp