Leadership News Hausa:
2025-04-20@22:58:39 GMT

An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

Published: 28th, March 2025 GMT

An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

“Jami’an ‘yansanda da ke ofishin ‘yansanda, Mayo Belwa, sun isa wurin, inda nan take suka garzaya da wanda abin ya shafa zuwa asibitin Cottage, Mayo-Belwa, domin  kokarin ceton ransa, amma abin takaici, an tabbatar da mutuwarsa a lokacin da ya ke karvar magani.”

Kakakin rundunar ‘yansandan ya ce, ya yi saurin shiga tsakanin wanda ake zargin da matasa suka kama shi domin cetonsa daga hannun matsan inda aka garzaya da shi asibiti.

Ya ci gaba da cewa wasu matasa a yankin da lamarin ya faru sun bi sawu inda suka kama daya daga cikin wadanda ake zargin ’yan fashi da makami ne kuma suka damke shi.

Ya gargadi mazauna jihar kan yin yin hukuncin nan na daukar doka a hannunsu tare da bukatar su da su kai rahoton duk wani abu da ya faru ga ‘yansanda.

“A bisa wannan karfi, daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Umar SNU, wasu fusatattun matasa ne suka bi sawun sa, inda suka yi ta kai ruwa rana kafin ‘yan sanda su kubutar da shi, sannan aka garzaya da shi asibiti domin kula da lafiyarsa, inda a yanzu ya taimaka wajen gudanar da bincike.

“Kwamishanan ‘yansanda, Dankombo Morris, ya yi Allah-wadai da wannan ta’addancin da kakkausar murya, sannan ya bayar da umarnin gudanar da sahihin bincike don tabbatar da an gurfanar da wadanda suka aikata laifin gaban kotu.

“Ya kuma gargadi jama’a da su daina daukar doka a hannunsu, ya kuma bukace su da su bar doka a kodayaushe ta yi aikinta, kuma su ci gaba da tafiyar da ayyukansu yadda ya kamata, rundunar ‘yansandan ta bukaci mazauna yankin da su yi taka-tsan-tsan tare da kai rahoto ga ofishin ‘yansanda mafi kusa,” in ji Nguroje.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a watan Disambar 2024 cewa wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun kai hari a unguwar Atan-Ota da ke karamar hukumar Ado-Odo/Ota ta jihar Ogun inda suka kashe wani jami’in tsaro da ke gadin wata karamar mota a yankin yayin da suka tsere da wata babbar mota da aka ajiye a dajin.

Wakilinmu ya samu labari daga wani mazaunin unguwar cewa wata mai sayar da abinci an gano gawarta a daji babu rai, inda aka yi masa fyade tare da daure ta a wata kusurwa.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi

An shiga ruɗu da fargaba a garuruwan ƙasar Chadi da dama, sakamakon jita-jita da kafofin sada zumunta na yanar gizo ke yaɗawa cewa wasu matsafa na satar al’aurar maza.

Tun daga birnin Moundou da ke kudancin kasar da lamarin ya fara samun asali, inda wasu matasa hudu suka yi ikirarin cewa an sace musu al’aurarsu ta hanyar bakar tsafi, na yaduwa kamar wutar daji a wasu manyan biranen ƙasar Chadi.

Sakamakon jita-jita da bidiyoyi iri-iri da ake yadawa a shafukan sada zumunta, duk da cewa ba a tabbatar da wannan zargi a likitanci ko a hukumance ba, lamarin ya bazu tare da tada hankula har a tsakiyar N’Djamena, babban birnin kasar, inda wasu fusatattun mutane suka yi yunkurin kashe wani mutum wanda suka zarga da sace al’aurar wasu yara maza uku bayan ya yi musabaha da su, sai dai ya tsira da ransa sakamakon shiga tsakani da ’yan sanda suka yi, amma ya ji jiki da ɗan karen duka.

Babu tushe a zahiri

A yayin da ake fuskantar wannan al’amari wanda a halin yanzu girmansa na iya haifar da hargitsi na zaman lafiyar jama’a, gwamnati ta yanke shawarar tashi tsaye don ƙoƙarin kawo karshensa.

Kakakin gwamnatin Chadi, Gassim Cherrif ya ce lamarin na neman wuce gona da iri, domin kuwa ana kai wa mutane hari tare da jikkata da dama saboda zargi marasa tushe a zahari, yana mai cewa gwamnati ba za ta zuba ido tana gani har lamarin ya girma ba, ta yadda mutane ke ɗaukar doka da hannunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • Hyda Ghaddar: Mai Son Horar Da ‘Yanmatan Kano Kwallon Kafa
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 8 Kan Zargin Kashe Jariri A Borno
  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya