ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH
Published: 28th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta kammala gyara wata cibiya don kula da masu fama da shan miyagun ƙwayoyi a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH) da ke Kano, tare da miƙa ta ga asibitin domin amfanin jama’a.
Jami’in ECOWAS mai kula da shirin hana yawaitar shan miyagun ƙwayoyi, Dokta Daniel Akwasi Amankwaah, ya ce wannan cibiya na daga cikin ƙoƙarin ƙungiyar wajen rage yawaitar shan ƙwayoyi da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga masu buƙata.
A yayin bikin miƙa cibiyar, Dokta Amankwaah, ya jaddada aniyar ECOWAS na yaƙi da matsalar shan miyagun ƙwayoyi, inda ta ce duniya ta ɗauki wannan matsala a matsayin wata babbar barazana ga lafiya da zamantakewa.
Ya bayyana cewa bayanan da Hukumar Bincike kan Amfani da Miyagun Ƙwayoyi a Yammacin Afirka (WENDU), ta fitar daga 2018 zuwa 2023 sun nuna ƙaruwar masu shan miyagun ƙwayoyi a yankin, duk da ƙarancin wuraren kula da su.
Saboda haka, ECOWAS ta ƙaddamar da wani shiri tun a 2019 domin taimaka wa membobints wajen kafa ko gyara cibiyoyin kula da masu shan miyagun ƙwayoyi.
Ya zuwa yanzu, an kammala cibiyoyi takwas a ƙasashe shida, inda Najeriya ta samu guda huɗu, yayin da ake ci gaba da aikin wasu uku.
Dokta Amankwaah, ya ce kammala wannan cibiya a AKTH zai taimaka wajen kula da marasa lafiya ta hanyar dabarun kiwon lafiya, wanda zai rage illar shan miyagun ƙwayoyi tare da inganta rayuwar jama’a.
Kwamandan Hukumar NDLEA a Kano, Ahmed Idris, ya ce wannan cibiya wata babbar nasara ce a yaƙi da shan miyagun kwayoyi.
Ya yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomi domin cimma gagarumin nasara.
Shi ma Shugaban AKTH, Abdurrahman Abba Sheshe, ya yaba da wannan tallafi, inda ya ce cibiyar ba kawai al’ummar Kano za ta taimaka ba, har da maƙwabtan jihohi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ECOWAS Miyagun ƙwayoyi shan miyagun ƙwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Kada Kanawa su bari rigingimun siyasa su hana su zaman lafiya — Shettima
Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya shawarci Kanawa kan kada su bari bambance-bambancen aƙidu na siyasa su zama silar hana su zaman lafiya da haɗin kai.
Ya faɗi hakan ne a jawabinsa lokacin da ya je yi wa Shugaban APC na Kano, Abdullahi Abbas, ta’aziyar rasuwar mahaifinsa — Galadiman Kano, Abbas Sunusi.
Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu? An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar ChadiShettima ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai, yana mai bayyana Kano a matsayin madubin Arewacin Nijeriya.
Yayin da yake nanata muhimmancin zaman lafiya, ya bayyana cewa kada a yi sake da Kano, inda ya buga misali da yadda rashin zaman lafiya ya ɗaiɗaita Jihar Borno.
Shettima ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a fannin siyasa da su ajiye banbancin aƙidu, su bai wa ci gaban Kano fifiko a kan komai.
Ya tunatar da cewa Jihar Kano wata cibiya da kusan duk jihohin Arewa suka kewaye kuma ta zama tamkar wata ƙofa da ta zama mahaɗar jihohin
“Idan za ka je Borno ko Bauchi ko Sakkwato, dole ne sai ka bi ta Kano. Saboda haka Kano jiha ce ta kowa.
Aminiya ta ruwaito cewa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya yi Mataimakin Shugaban Ƙasar rakiya a yayin ziyarar ta’aziyyar da ya kai gidan marigayi Galadiman Kano.