Aminiya:
2025-03-31@08:24:28 GMT

Ɓarayin kekunan ɗinki sun shiga hannu a Borno

Published: 28th, March 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta kama wasu matasa uku da ake zargi da satar kekunan ɗinki guda 19 a cibiyar koyon sana’a ta Dala Lawanti da ke Maiduguri.

A cewar ’yan sanda, wani mai gadi a cibiyar, Kaka Modu Mustapha, mai shekaru 34, ya haɗa baki da wasu matasa biyu – Bukar Mustapha mai shekaru 16 da Ibrahim Mohammed mai shekaru 17 – domin aikata satar a ranar 22 ga wata Maris, 2025.

ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio

Kakakin rundunar, SP Nahum Kenneth Daso, ya ce jami’an ’yan sanda daga yankin Bulumkutu, sun samu rahoto game da satar, inda suka gudanar da bincike tare da kama waɗanda ake zargin, ciki har da mai gadin cibiyar.

Ya ce an samu nasarar ƙwato kekunan ɗinki guda shida daga cikin 19 da suka sace, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano sauran guda 13.

SP Daso, ya buƙaci al’ummar jiharda su kasance masu kula tare da kai rahoton duk wani abun zargi ga jami’an tsaro domin daƙile aikata laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Cibiyar Koyon Sana o i

এছাড়াও পড়ুন:

Abubuwan da Za ki Runguma domin Burge Mijinki

ki kiyaye magungunan na bature da wadanda ba su da inganci. Jiki ba a abin wasa bane kada garin gyaran gira a rasa ido. ki gode wa Allah a yadda ya halicce ki duk yadda kike akwai wacce ba ta kai ki ba. Halittarki da kike ta korafi, wata kuma shi take kwadayin samu.

Ki nemi hanyoyin na halal don inganta jikinki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Abubuwan da Za ki Runguma domin Burge Mijinki
  • Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo
  • Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno
  • Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya
  • Kisan ’yan Arewa a Edo ya tayar da ƙura
  • Kwankwaso Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Arewa A Edo, Ya Buƙaci A Yi Adalci
  • ECOWAS ta gyara cibiyar magance shan miyagun ƙwayoyi a AKTH
  • An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa