Kwankwaso ya buƙaci hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike tare da tabbatar da cewa an hukunta masu laifin.

“Ina kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike a kan wannan lamari mai tayar da hankali tare da tabbatar da an hukunta masu hannu a ciki,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan, da gwamnatin Kano da sauran jihohin da abin ya shafa, tare da yin addu’ar Allah Ya jiƙansu.

Kisan ya haifar da cece-ku-ce kan hatsarin da ke tattare da ɗaukar doka a hannu, tare da buƙatar a ƙara inganta tsaro don hana irin haka faruwa a gaba.

Jagororin siyasa da na al’umma da dama sun goyi bayan kiran da Kwankwaso ya yi na neman adalci, tare da buƙatar gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa a kan waɗanda suka aikata wannan ta’asa.

Yayin da bincike ke ci gaba, ana ci gaba da matsin lamba kan hukumomin tsaro don tabbatar da cewa an yi adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Arewa Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Kamo Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo

Shugaban ƙasar ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, da shugabannin al’ummar Uromi bisa matakin da suka ɗauka domin daƙile yiwuwar tashin hankali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Azumin Sitta Shawwal a Musulunci
  • Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo
  • Kisan ‘Yan Arewa 16 A Jihar Edo: Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Nemi Adalci
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Kamo Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Kisan ’yan Arewa a Edo ya tayar da ƙura
  • Gwamnatin Edo Za Ta Binciki Kisan Matafiya ‘Yan Arewa A Jihar