Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
Published: 28th, March 2025 GMT
A cewar shugabannin Ƙwadago, dole ne a sauya irin wadannan lamari don kare mutuncin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya.
Sun jaddada wahalar da dokar ta-ɓaci ta haifar wa ma’aikatan kananan hukumomi, da yawa daga cikinsu har yanzu ba su karɓi albashinsu ba.
Sanarwar ta lura cewa hana albashin ma’aikata ya jefa su cikin matsin tattalin arziki, musamman ma a irin wannan lokaci da ake samun tsadar rayuwa a cikin kasar nan.
Ƙungiyar Ƙwadago ta yi gargadin cewa dokar ta-vaci na iya haifar da mummunan sakamako na tattalin arziki, tana mai jaddada muhimmancin da Jihar Ribas ke da ita ga tattalin arzikin Nijeriya da yankin Neja Delta gaba daya.
Ta ce da ma can kasar nan ta riga ta fuskanci hauhawar farashi, raguwar darajar naira, tsadar musayar canji, rashin aikin yi da tsadar rayuwa, rashin kwanciyar hankali a Jihar Ribas na iya kara ta’azzara halin da ake ciki a duk fadin kasar nan.
Sanarwar ta kuma nuna cewa rashin tabbas na siyasa da dokar ta-ɓaci ta haifar ya kori masu saka hannun jari wadanda suka nuna sha’awar zuba hannun jari a tattalin arzikin jihar.
“Wannan asarar saka hannun jari yana lalata kudaden shiga na cikin gida na jihar (IGR), kuma zai yi tasiri na dogon lokaci a ci gaban tattalin arziki da kuma damar samar da ayyukan yi a yankin.
“Duk da cewa mun amince da bukatar kiyaye doka da oda, dole ne a aiwatar da irin wadannan matakai a cikin tsarin kundin tsarin mulkin Nijeriya.
Dakatar da zaɓaɓɓun jami’ai da lalata tsarin biyan albashin ma’aikata ya keta hakkoki dan’adam wanda zai iya ta’azzara rashin tsaro da kalubalen tattalin arziki.
“Ya kamata gwamnatin tarayya ta ba da fifiko ga tsaro da jin dadin ‘yan kasa a kan muradun siyasa.
“Duk wata hanyar mulki da ke sadaukar da jin dadin ma’aikata don ayyukan siyasa zai kara tashin hankali da rashin kwanciyar hankali ga al’umma,” in ji ƙungiyar ƙwadago.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Dokar Ta ɓaci Ƙungiyar Ƙwadago tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna
Akwai yiwuwar Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa wata dokar Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA) a wasan gasar La Liga wanda ta doke Osasuna.
Rahotanni na cewa ƙungiyar Osasuna za ta shigar da ƙorafi kan wasan da Barcelona ta doke ta da ci 3-0, saboda zargin saɓa dokar FIFA kan amfani da ɗan wasan da bai cancanta ba.
Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a ZamfaraA jiya Alhamis ce Barcelona ta karɓi baƙuncin Osasuna a wani kwantan wasa na gasar La Liga, inda to doke baƙin nata da ci 3-0.
Wannan nasarar ta bai wa Barcelona damar yin zaman faɗi da tazarar maki 3 a saman teburin La Liga da jimillar maki 63, bayan buga wasanni 28.
Sai dai wasan ya bar baya da ƙura, saboda Osasuna na zargin Barcelona ta karya wata dokar FIFA kan amfani da wani ɗan wasa yayin karawar.
Osasuna na zargin cewa ɗan wasan baya na Barcelona, Inigo Martinez wanda ɗan asalin Sifaniya ne, bai cancanci buga wasan ba.
A kakar bana, tauraruwar Martinez na haskawa tun bayan zuwan sabon koci Hansi Flick ƙungiyar, wanda ya sa ɗan wasan ya samu kiranye daga tawagar ƙasarsa Sifaniya a watan nan.
Sai dai ɗan wasan ya samu rauni a gwiwa, lamarin da ya tilasta masa baro tawagar Sifaniya da ke buga gasar UEFA Nations League, inda aka maye gurbinsa da ɗan wasan Bournemouth, Dean Huijsen.
Sai dai kuma bayan ya baro tawagar ta Sifaniya, Martinez ya dawo ƙungiyarsa ta Barcelona, inda ya buga wasan da suka yi nasara kan Osasuna a ranar Alhamis.
Shafin Goal ya ambato wata jaridar wasanni ta Sifaniya, Diario Sport, na cewa Osasuna na duba yiwuwar shigar da ƙorafi kan Barcelona saboda zargin taka dokar FIFA dangane da saka ɗan wasan da ya baro tawagar ƙasarsa.
Osasuna na ganin cewa, bai kamata a ce Martinez ya buga wasan ba saboda dokar FIFA ta ce ‘yan wasan da suka baro tawagar ƙasarsu ba za su buga wa ƙungiyarsu wasa ba har sai bayan aƙalla kwanaki biyar, face idan hukumar ƙwallo ta amince masa ya buga