Da safiyar yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da wakilan da suka fito daga sassan masana’antu da cinikayya na kasa da kasa a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Xi ya jadadda cewa, a cikin shekaru 70 da kafuwar jamhuriyar jama’ar Sin musamman ma cikin shekaru 40 da aiwatar da manufar yin kwaskwarima a gida da bude kofa ga waje, Sin ta cimma gaggaruman nasarori wajen samun saurin bunkasuwar tattalin arziki da dorewar walwalar al’umma dogaro da jagorancin jam’iyyar kwaminis ta Sin wato jKS da kokarin al’ummar Sinawa cikin hadin kai, kuma ba za a raba wadannan nasarori da taimakon da kasashen duniya ke ba ta ba, cikin hadda gudunmawar da kamfanonin ketare dake kasar Sin suke bayarwa.

Kwarewar Kasar Sin Da Ci Gabanta A Fannin Fasaha Na Da Muhimmanci Wajen Inganta Zamanantar Da Afirka ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro

Ban da wannan kuma, Xi ya ce, kasancewarta muhimmiyar kasar dake taka rawar gani da tabbatar da bunkasuwar tattalin arzikin duniya, yanzu kasar Sin tana kokarin zamanantar da kanta a duk fannoni. Ya ce bude kofa wata manufa ce mai tushe da Sin take aiwatarwa, kuma tana kokarin kara inganta wannan tsari a kai a kai, da habaka bude kofa a bangaren ka’idoji da manufofi da ma’auni da sauransu. Ba shakka Sin za ta habaka bude kofarta, da nace wa ga manufar amfani da jarin waje. Hakan ya sa, Sin ta zama wuri mai kyau dake samar da yanayi mai tsaro da inganci ga jarin waje a ko da yaushe.

Shugabanni da manyan jami’an kamfanonin kasa da kasa fiye da 40 sun halarci taron. Sun kuma nuna cewa, kimiyya da fasaha na taka rawar gani ga sauya salo da daga matsayin masana’antun kasar Sin. Matakin da zai taimaka wajen samun bunkasuwa mafi inganci da dorewa, kuma shi ya sa suke ganin, tattalin arzikin Sin na da makoma mai haske. Kazalika, sun ce Sin ta rika habaka bude kofarta ga ketare duk da cewa ana fama da manufar kariyar cinikayya a duniya, abin da ya baiwa tattalin arzikin duniya tabbaci, har ya sa Sin ta zama tabbataccen wurin da ya fi dacewa da zuba jari. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba

A cewar shugabannin Ƙwadago, dole ne a sauya irin wadannan lamari don kare mutuncin tsarin dimokuradiyya a Nijeriya.

Sun jaddada wahalar da dokar ta-ɓaci ta haifar wa ma’aikatan kananan hukumomi, da yawa daga cikinsu har yanzu ba su karɓi albashinsu ba.

Sanarwar ta lura cewa hana albashin ma’aikata ya jefa su cikin matsin tattalin arziki, musamman ma a irin wannan lokaci da ake samun tsadar rayuwa a cikin kasar nan.

Ƙungiyar Ƙwadago ta yi gargadin cewa dokar ta-vaci na iya haifar da mummunan sakamako na tattalin arziki, tana mai jaddada muhimmancin da Jihar Ribas ke da ita ga tattalin arzikin Nijeriya da yankin Neja Delta gaba daya.

Ta ce da ma can kasar nan ta riga ta fuskanci hauhawar farashi, raguwar darajar naira, tsadar musayar canji, rashin aikin yi da tsadar rayuwa, rashin kwanciyar hankali a Jihar Ribas na iya kara ta’azzara halin da ake ciki a duk fadin kasar nan.

Sanarwar ta kuma nuna cewa rashin tabbas na siyasa da dokar ta-ɓaci ta haifar ya kori masu saka hannun jari wadanda suka nuna sha’awar zuba hannun jari a tattalin arzikin jihar.

“Wannan asarar saka hannun jari yana lalata kudaden shiga na cikin gida na jihar (IGR), kuma zai yi tasiri na dogon lokaci a ci gaban tattalin arziki da kuma damar samar da ayyukan yi a yankin.

“Duk da cewa mun amince da bukatar kiyaye doka da oda, dole ne a aiwatar da irin wadannan matakai a cikin tsarin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Dakatar da zaɓaɓɓun jami’ai da lalata tsarin biyan albashin ma’aikata ya keta hakkoki dan’adam wanda zai iya ta’azzara rashin tsaro da kalubalen tattalin arziki.

“Ya kamata gwamnatin tarayya ta ba da fifiko ga tsaro da jin dadin ‘yan kasa a kan muradun siyasa.

“Duk wata hanyar mulki da ke sadaukar da jin dadin ma’aikata don ayyukan siyasa zai kara tashin hankali da rashin kwanciyar hankali ga al’umma,” in ji ƙungiyar ƙwadago.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Sin Da Laberiya Sun Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Ta Fuskar Tattalin Arziki Da Fasaha 
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
  • Shugaban CMG Ya Gana Da Ministar Raya Al’adu Ta Rasha
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba