HausaTv:
2025-04-20@12:12:59 GMT

Miliyoyin mutane sun gudanar da jerin gwanon ranar Qudus

Published: 28th, March 2025 GMT

Miliyoyin al’umma daga sassa daban daban na duniya sun gudanar da jerin gwanon zagayowar ranar Kuds ta duniya wacce ta gudana yau.

An dai kebance ranar ce domin nuna goyan baya ga al’ummar falasdinu, kuma ana gudanar da ita ne a ko wacce Juma’ar karshe ta watan ramadana bisa fatawar jagoran juyin juya halin musulinci na Iran Ayatollah Khumeiny.

A Iran ma kamar sauren sassan duniya jama’a sun fito kan tituna domin gudanar da bukukuwan ranar Qudus ta duniya, inda suke bayyana goyon bayansu ga Falasdinawa tare da yin tir da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a zirin Gaza.

An kuma yi irin wannan gangamin a kasashe da dama na yankin yammacin Asiya da suka hada da Iraki da Yemen da Lebanon da kuma wasu da dama a fadin duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango

Bala’in Kogin Congo: Kwale-kwale ya kama wuta, ya kashe mutane 143

A wani mummunan lamari da ya afku a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, akalla mutane 143 ne suka mutu, wasu da dama kuma suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kama da wuta a kogin Kongo da ke arewa maso yammacin kasar.

Akalla mutane 143 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kama da wuta a kogin Kongo da ke arewa maso yammacin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, kamar yadda majiyoyin hukuma suka bayyana.

“An gano rukunin farko na gawarwakin mutane 131 a ranar Laraba, kuma an sake gano wasu 12 a ranakun Alhamis da Juma’a,” ‘yar majalisar wakilan kasar Josephine Pacific Lokomo ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

A nasa bangaren, Joseph Lokondo, shugaban kungiyoyin farar hula na yankin, ya bayar da bayanai kan adadin wadanda suka mutu na wucin gadi, wanda ya kai mutane 145.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne
  • Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da  Saudiyya
  • Iran Tana Daukan Tattaunawarta Da Amurka Da Muhimmanci Don Neman Warware Takaddamar Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • An Fara Bada Horo Ga Masu Horas da Maniyatan Bana A Jigawa
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi