Aminiya:
2025-03-31@13:40:52 GMT

Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno

Published: 29th, March 2025 GMT

Ƙungiyar Jama’atul Nasrul Islam (JNI) , ta raba kayayyaki da sauran kyatuttukan Sallah ga marayu 50 gabanin bikin Sallah ƙarama a garin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

An gudanar da bikin ba da tallafin ne a harabar makarantar sakandare ta Bulabulin da ke birnin na Maiduguri.

Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin Nijeriya Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna

Da yake jawabi a wajen taron, mataimakin daraktan kungiyar JNI reshen Maiduguri, Malam Ibrahim M.

Bello, ya jaddada muhimmancin tallafa wa mabuƙata, yana mai jaddada cewa wannan shi ne babban burin ƙungiyar.

Ya buƙaci waɗanda suka samu tallafin da su yi amfani da kyaututtukan domin biyan buƙatunsu.

A nasa jawabin, mataimakin sakataren ƙungiyar, Abubakar Abdullahi, ya ce sun yi hakan ne da nufin sanya farin ciki da jin dadi ga yara marasa galihu a lokacin bukukuwan Sallah.

Ƙungiyar ta JNI ta himmatu matuƙa wajen taimaka wa mabuƙata, musamman marayu da ba su da abin dogaro da kai in ji Abubakar.

Ya kara bayyana cewa, an zabo waɗanda suka samu tallafin ne bisa sharuɗan da hukumar gudanarwar ƙungiyar ta gindaya.

A cewarsa, ƙungiyar ta shafe sama da shekaru goma tana gudanar da irin waɗannan ayyuka na agaji.

Abdullahi ya kuma yi kira ga iyaye, hukumomin gwamnati, da shugabannin masana’antu da su haɗa hannu wajen ganin an samu sauƙaƙa rayuwar marayu.

Ya yi nuni da cewa, wannan ƙoƙari na haɗin gwiwa zai taimaka matuƙa wajen tallafa wa yara masu rauni da kuma inganta fahimtar al’umma dangane da zamantakewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno kayan Sallah Marayu

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja

Rahotanni daga Najeriya na cewa mutane 20 ne suka mutu sakamakon hatsaniyar da aka samu tsakanin sojoji da masu jerin gwanon ranar Kudus ta duniya a Abuja fadar mukin Najeriya.

Hotunan faifan bidiyo sun nuna yadda masu zanga-zangar ke neman mafaka yayin da karar harbe-harbe ke kara kamari a kusa da su.

An ce an kai gawarwakin mutanen goma sha hudu zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Ana gudanar da tattakin ranar Qudus ta duniya duk shekara a ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan domin nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Najeriya : An samu hargitsi a yayin jerin gwanon ranar Kudus a Abuja
  • Dalilin da Aminu Bayero ba zai iya jagorantar hawan Sallah ba — Kurawa
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Bada Tallafin Noman Rani Ga Manoma 300
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma 
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba