Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma
Published: 29th, March 2025 GMT
Ma’aikatar Ayyuka da Samar da Kayayyakin More Rayuwa, tare da hadin gwiwar First Impression Communication Limited, ta shirya wani taro kan shirin Samar da Ruwa Mai Tsafta a Birane da Karkara da Tsabtace Muhalli da Kiwon Lafiya (SURWASH) da ya gudana a Arewa House, a Kaduna.
Da yake bude taron, Kwamishinan Ayyuka da Samar da Kayayyakin More Rayuwa, Dakta Ibrahim Hamza, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar na magance matsalar karancin ruwa a jihar.
Kwamshinan wanda Mataimakin Daraktan Albarkatun Ruwa, David Roven Aliyu ya wakilta, ya bayyana kokarin da gwamnati ke yi, ciki har da gina rijiyoyin burtsatse a wasu al’ummomi domin inganta tsaftar muhalli da kiwon lafiya.
“Shirin SURWASH na Najeriya wani shiri ne da Asusun Bada Lamuni na Duniya (World Bank) ke daukar nauyinsa da dala miliyan 700 domin inganta ayyukan WASH a jihohi bakwai na Najeriya, ciki har da Kaduna.
Manufar shirin ita ce samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane miliyan shida da kuma inganta tsaftar muhalli ga mutane miliyan 1.4.
Dakta Hamza ya bayyana cewa an ware kananan hukumomi guda shida a Jihar Kaduna wanda suka hada da —Soba, Igabi, Chikun, Jaba, Jema’a, da Sabon Gari—domin tabbatar da su sun samu tsaftatacen Ruwa Sha a yankunan su.
“Da zarar wadannan yankuna sun cika ka’idojin da ake bukata, za a kara zabar karin kananan hukumomi guda bakwai domin shirin,” in ji shi.
Ya bukaci jama’a su kare kayayyakin tsafta da kiwon lafiya da gwamnati ta samar domin su dade ana amfana da su.
A nasa jawabin, Shugaban Shirin SURWASH na Kaduna, Mista Esau Ambinjah, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar al’umma wajen kare rijiyoyin burtsatse da sauran kayayyakin tsafta.
Ya kuma bayyana cewa an riga an zabi kananan hukumomi guda bakwai—Sanga, Makarfi, Kudan, Zaria, Kaduna ta Arewa, Kaduna ta Kudu, da Zangon Kataf—domin shirin SURWASH.
A nata jawabin, Shugabar Kungiyar Mata Musulmi ta Najeriya (FOMWAN), Amira Hafsatu Musa Isa, ta bada shawarar cewa ya kamata a sanya abun da ya dace da al’adu da addini a cikin shirye-shiryen wayar da kai.
Haka kuma, Shugabar Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen mata a Kaduna, Bishop Eister Yawai, ta bukaci a fadada yakin wayar da kan SURWASH zuwa wuraren addinai.
Ta bayyana cewa samun tsaftataccen ruwa yana da matukar muhimmanci wajen hana yaduwar cututtukan da ke da nasaba da ruwa.
Ta kuma bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su kara kaimi wajen magance matsalar karancin ruwa a wasu al’umomi.
Wanda ya gabatar da shirin, Yusuf Idris, ya gabatar da sanarwar wayar da kai na SURWASH da aka fassara cikin Hausa da turanci, inda mahalarta suka gabatar da ra’ayoyinsu domin inganta shirin.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Ruwan Sha
এছাড়াও পড়ুন:
Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya musanta cewa akwai tsamin dangantaka tsakaninsa da Gwamnatin Sakkwato.
Ana iya tuna cewa bayan karɓar akalar jagoranci ne Gwamna Ahmed Aliyu ya yi wa Dokar Masarautar Sakkwato gyaran fuska tare da sauke wasu sarakunan gargajiya, lamarin da aka riƙa raɗe-raɗin wani yunƙuri ne tsige shi kansa Sarkin Musulmin.
Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wutaSai dai da yake jawabi a saƙonsa na barka da sallah, Sarkin Musulmi ya ce “ba wata rashin jituwa ko faɗa a tsakaninmu.
“Muna aiki tare a koyaushe. Aikinmu mu taimaka wa gwamnatin [Sakkwato] kan shirye-shiryen da ta ɗauko domin ciyar da jama’a gaba.”
Ya yi kira ga al’ummar musulmi da su ci gaba da yi wa shugabanni addu’a domin samun nasara wajen sauke nauyin jama’a da rataya a wuyansu.
Kazalika, Alhaji Sa’ad ya ce karantarwar addini da aka samu a watan Azumi mai albarka abu ne da ya kamata a riƙe a sanya cikin aiki.
“Mu ƙara ɗaure ɗamara kar mu koma gidan jiya wajen aikata saɓon Allah. Mu dage da yin ibada kar a ja baya. Sannan mu riƙa yi wa shugabanni addu’a.
“Ku kuma shugabanni ku ji tsoron Allah cikin jagoranci. Idan za a yi ayyukan jama’a kar a ji tsoron kowa sai Allah,” in ji Sarkin Musulmi.
Sarkin ya yi kira ga jami’an tsaro da su ktara ƙaimi wajen magance matsalar tsaro domin a cewarsa har yanzu akwai sauran aiki a ba iya Jigar Sakkwato kaɗai ba.