A yammacin yau Juma’a ne ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai a birnin Lhasa na jihar Xizang wato Tibet, inda aka fitar da “Takardar bayanin ci gaban sha’anin kare hakkin dan Adam a Tibet a sabon zamani”.

Takardar ta yi nuni da cewa, a ko da yaushe, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin kasar suna mai da hankali kan ayyukan da suka shafi Xizang, kuma suna ci gaba da kyautatawa da raya tsarin mulkin Xizang, da daukar matakai masu inganci don raya tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama’a, da kawo alheri ga jama’a, da inganta hadin kai da ci gaban kabilu, da kuma kare hakkin dan Adam na dukkan kabilun jihar Xizang.

Ta kara da cewa, a halin yanzu, jihar Xizang ta samu kwanciyar hankali a bangaren siyasa, da hadin kan kabilu, da bunkasar tattalin arziki da zamantakewar al’umma, lamarin da ya haifar da wani abin al’ajabi na kare hakkin dan Adam a tudun dusar kankara.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Sunana Naja’atu Baffa Jihar kaduna:

Ni dai a gaskia ban son akwai wani anko da za ai wannan sallar ko babu ba. Ina son saka takalmi mai dan tudu ba sosai ba, sai mayafi blue black, sai atamfa ta riga (half bubu) da ‘skirt’, sai sarka da dankunne da Awarwaro ‘silver’. Ina sha’awar cin Snacks irinsu meatpie, samosa, doughnut da kuma cake, sai kuma Yoghurt mai inibi. Ina son in ziyarci kanwar babata wacce take a cikin garin Adamawa.

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To batun shidimar sallah sai mu ce Alhamdullilah domin duk tanadin da mutum yayi sai ya kare, duba da yadda kayayyakin suturu ko tufafi suke tsada don haka sai mutum yayi amfani da abun da ya samu, domin gudanar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali ya fi komai dadi. To magana ta gaskiya shadda ita ce kalar kayan da zai fi yawa domin ita shadda ba a daina yayinta kuma tana daga cikin kalar suturar da duk mai hali ko sukuni zai so ya dinka, amma wasu kuma za su dinka yaduka domin kowa da irin kalar suturar da ta fi burge shi. To ni dai nafi sha’awar farin kaya musamman yadda manyan kaya ma’ana riga, binjima da wando da kuma hula fara wannan sune kalar suturar dana fi so musamman lokacin zuwa idi. Batun babu zabi duk wanda na samu zan ci, amma nafi son biskin alkama da miyar yakuwa ko jar miya. To da farko dai Masallacin idi shi ne guri na farko, sannan kuma sai ziyarce-ziyarce gidajen ‘Yan’uwa da abokan arziki.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar kaduna:

An yi wa sallah tanadi da dama kamar kayan da za a sa, Lalle, kitso, da sauransu. Bana tunanin gaskiya akwai wani anko da aka fitar domin a halin yanzu ko wa abin da Allah ya hore mai zai saka. Ina son saka shadda mai ‘stones’, ina son cin funkaso, tuwon shinkafa da miyar Agushi wadda ta ji ganda, kaji da kayan ciki, sai lemon ginger, sai farfesun zallar naman zabi.

Sunana Anas Bin Malik Achilafia Yankwashi A Jihar Jigawa:

Ana yin tanadi wa bukukuwan Sallah da yawa, amma dai ni kam babu tanadin dana yi wa sallar bana, batun anko  ko yayin kayan da ake siya, ni dai kam har yau ban lura ba, amma dai bana Iyalai na suna sha’awar Shadda, kuma gaskiya ba na ina sha’awar cin sakwara da hadadden lemu (Ubangiji Allah ka kara hore mana). A bisa al’ada kuma muna kaiwa ‘yan’uwa da abokan arzuka ziyara, tare da taya murnar kammala ibada. Ubangiji Allah karva mana ibada, ya sa mun dace.

Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Tanadin dana yi wa wannan sallah shi ne ina so ta same ni cikin koshin lafiya da kuma ‘yan canji a cikin aljihuna. Wannan shekarar ta zo da son yin wankan shadda wato shampoo ita ce kowacce saurayi ko budurwa take/yake son sakawa duk da tsadar rayuwa da muke fama da ita. Ina sha’awar saka farar sutura ko shadda da farar hula a lokacin tafiya sallar idi. Abincin da nake muradin ci sh ine funkaso da jar Miya da naman kaji. Ina son kai ziyara zuwa gidan ‘Yan’uwa da abokan arziki in sha Allah.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar kano Rano LGA:

Babban tanadi shi ne Allah ya nuna mana ita muna raye da koshin lafiya. Haka ne kam duk da ana cikin yanayi ba za a rasa wadanda suka yin ba amma mu masu iyali iya yaranmu da iyayensu muka samu muka yi wa. da son samune ni dai sabuwar shadda fara idan kuwa ba ita ba to na sami koda koriya ce ko yadi shi ma fari ko koren. Waina da kunun daka ko na alkama da miya. Bayan dawowa daga sallar idi zan je gidan mahaifina da kuma gidan surukaina sai kuma na ‘yan’uwa da abokaina na kusa domin kara sada zumunci. Allah ya karvi ibadunmu.

Sunana Aisha T. Bello Jihar kaduna:

Sallah bikin daya rana in ji masu magana, a gaskiya na yi ma wannan sallah tanadi babba in Allah ya sa muna da rabon gani. Zan sanyaya raina ta samar da abun da na fi so a ci da sha, zan kai ziyara, zan je kallon hawan sallah, sannan zan kikkira ‘yan’uwa domin taya su barka da sallah da yardar Allah. A gaskiya bana jin wannan sallar akwai wani tanadi na anko kamar kullum, duba da yanayin rayuwa ana ta abun ci da sha ne, ina sha’awar saka doguwar riga da salla in sha Allah, sannan in sa babban mayafi in halarci sallar idi. In Allah ya ba ni dama ina so in kai ziyara jihar katsina don ganin dangina da ‘yan’uwa in sha Allah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Ba Za A Iya Dakile Ci Gaban Hakkin Dan Adam Na Xizang Da Kowace Irin Karya Ba
  • Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
  • An kashe mutum 10 a wani sabon hari a Filato
  • Kasar Sin Za Ta Zage Damtsen Kawo Sauye-sauyen Zamani A Masana’antar Kananan Kayayyaki