HausaTv:
2025-04-21@06:43:27 GMT

Sharhi: Taruka Da Gangamin Ranar Quds Ta Duniya 2025

Published: 29th, March 2025 GMT

A wannan Juma’a ce 28 ga watan Maris na shekarar 2025, aka gudanar da taruka da jerin wano na ranar Qudus ta duniya wadda ta zo daidai da ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan mai alfarma.

An gudanar da wadannan taruka da jerin gwano ne a kasashe daban-daban da suka hada da wasu kasashen musulmi da na larabawa, har da wasu da wasu daga cikin kasashn ymmacin duniya da kuma na Afirka, ta hanyar shirya gagarumin gangamin da ke jaddada aniyarsu ta tabbatar da al’ummar Palastinu ta samu hakkokinta da Haramtacciyar kasar Isra’ila ta haramta musu, tare da nuna cikakken goyon baya ga gwagwarmayarsu ta neman samun wadannan hakkoki nasu.

A safiyar Juma’ar ne aka fara gudanar da jerin gwano na ranar Qudus ta duniya a duk fadin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, inda aka samu halartar jama’a da dama karkashin taken “Muna ci gaba da cika alkawarin da muka dauka.” Mahalarta tarukan sun yi tattaki ne daga masallatai da manyan filaye a birane da kauyukan kasar zuwa wuraren da ake gudanar da Sallar Juma’a.

A birnin Mashhad da ke gabashin Iran, tun da sanyin safiya ne aka fara gudanar da jerin gwano a wani bangare na tarukan ranar Kudus da aka saba gudanarwa shekara-shekara.

A birnin Tehran fadar mulkin kasar ta Iran haka lamarin ya kasance, inda tun da jijjfin safiya dubun dubatar jama’a suka fara fita domin isa wurare da aka kebance domin taruwa, kamar yadda aka saba a kowace ana taruwa ne babban titin Inqilab, wanda titi ne da ya kai tsawon fiye da kilo mita goma a tsakiyar birnin Tehran, inda jama’a suka cika wannan titi makil a lokacin gudanar da jerin gwanon ranar Quds ta dunya.

A jajibirin ranar ta Quds Jagoran juyin juya halin Musulunci a Iran Sayyed Ali Khamenei ya bayyana cewa, tattakin ranar Kudus ta duniya na wannan shekara da yardar Allah zai kasance mafi girma a kan na sauran shekaru da suka gabata.

A cikin wani sakon da ya aike ta gidan talabijin a daren Alhamis, jagoran ya bayyana cewa, wannan rana a ko da yaushe wata alama ce ta hadin kai da karfin al’umma, yana mai bayyana yadda tattakin ke nuni da cewa al’umma na tare da gwagwarmaya a kan muhimman manufofinta na siyasa, da kuma tsayawa tsayin daka wajen kare hakkokin al’ummar Falastinu.

A kasar Iran dukkanin bangarori na al’umma suna halartar gangamin ranar Quds ta duniya, da hakan ya hada da mabiya addinai daban-daban, da sauran bangarori na al’umma da jami’an gwamnati da ‘yan kasuwa da ma’aikata da ‘yan siyasa da kuma malamai, inda suke haduwa a kan kalma guda guda da manufa guda daya, ita ce nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu, da kuma yin tir da Allawadai da zaluncin Isra’ila a kans, da kuma yin kira da babbar murya a kan wajabcin kare hakkokin wannan al’umma da ake zalunta tsawon shekaru aru-aru.

A sauran bangarori na duniya kuwa, an gudanar da irin wannan gangami da jerin gwano a kasashe daban-daban, yankin Jammu da Kashmir na kasar Indiya, an samu halartar dimbin jama’a da ke daga tutocin Falasdinawa da kuma hotunan masallacin al-aqsa, yayin da suke rera taken ‘Yanci ga Falasdinu.

A kasar Bahrain musamman a yankin Bilad al-Qadeem, mahalarta taron sun daga hotunan Sheikh Isa Qassim, Sheikh Ali Salman, da shahidi Sayyed Hassan Nasrallah, a matsayi alama ta gwagwarmaya da zaluncin Isra’ila da kuma nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu.

A kasar Yemen, kwamitin al-Aqsa, ya kebance dandalin Sabeen da ke babban birnin kasar Sanaa, tare da wurare sama da 400 a fadin larduna 14, a matsayin wuraren da aka gudanar da gagarumin gangami na ranar  Qudus.

Musulmi da kuma masu fafutukar ‘yanci da kare hakkokin bil adama a duniya suna gudanar da ranar Qudus ta duniya kowace shekara a ranar Juma’ar karshe ta Ramadan, inda suke shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga al’ummar Palastinu.

A wasu ƙasashe, ƙungiyoyin zamantakewa daban-daban-ciki har da masana da masu fasaha, suna aiki kafada da kafada don wayar da kan jama’a game da buƙatar tabbatarwa da kiyaye haƙƙin Falasɗinawa ta hanyar gudanar da taruka na kara wa juna sani da laccoci, baje kolin zane-zane, da tattara gudummawa da kayan agaji.

Baya ga sassa na kasashen gabas ta tsakiya da Asia, an gudanar da irin wannan taruka da gangami a wasu kasashen yammacin turai da Amurka da kuma Latin Amurka, da kuma wasu daga cikin kasashen nahiyar Afirka, da suka hada da Najeriya, Tanzania, Ghana, Senegal, Mali, Kenya, Afrka ta kudu da sauransu.

Ana gudanar da ranar Qudus ta duniya ne a ranar Juma’ar karshe ta watan Ramadan bisa kiran da Imam Khumaini ya yi, wanda shi ne ya jagoranci juyin juya halin Musulunci, sannan kuma yunkuri nasa na ayyana ranar Qudus ta duniya, yana a matsayin wani mataki na kare hakkokin al’ummar Palastinu da ‘yancinsu, bayan shafe tsawon shekaru suna cikin wahala da kangi da hijira da mamaye yankunansu, da kuma tuna da duniya irin wannan mawuyacin halin da Isra’ila tare da taimakon kasashen yammacin duniya suka jefa Falastinawa a ciki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ranar Qudus ta duniya da jerin gwano goyon baya ga kare hakkokin

এছাড়াও পড়ুন:

Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere

 

A shekaru 70 da suka wuce, kasashen yamma sun yi wa taron Bandung kallon taro na kasashe matalauta, amma kuma ga irin yadda ya haifar da kyakkyawan sakamako ga mikewar kasashen. A zamanin yau, lokacin da kasar Amurka ke ta kara kakaba harajin kwastam a kan sauran kasashen duniya, muna farin cikin ganin yadda kasashe masu tasowa ke hada kansu, da rike tsaronsu da ci gabansu a hannunsu, suna kuma rungumar akidun zaman lafiya da hadin gwiwa da bude kofa don tinkarar yadda kasashe masu karfi ke neman cin zalin kasashe masu karamin karfi da ma rashin tabbas da ake fuskanta a duniya. Yau da muke waiwayen taron Bandung, za mu gano cewa, ko-ba-dade-ko-ba-jima za mu ga bayan nuna fin karfi a tarihin wayewar kan dan Adam. (Lubabatu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ango ya tsere tare da surukarsa
  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe
  • Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • JAMB ta sauya ranar soma jarrabawar bana
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • Amurka Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadancinta Kimani 30 A Duniya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Za A Gudanar Da Zagaye Na Biyu Na Tattaunawar Iran Da Amurka A Birnin Roma Ne