Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
Published: 29th, March 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bakin kakakinta Dr. Isma’ila Baka’i, ta yi tir da sabbin hare-haren da HKI ta kai wa kasar Lebanon a daidai lokacin da ake bikin ranar Kudus.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na kasar ta Iran ya bayyana cewa; Abinda HKI ta yi keta tsagaita wutar yaki ne,wanda abin a yi tir da shi ne.
Haka nan kuma ya yi ishara da nauyin da ya rataya akan wuyan Majalisar Dinkin Duniya da kuma sauran kasashen da suke cikin sa-ido da ‘yarjeneniyar tsagaita wutar yaki, haka nan kuma ya yi kira zuwa ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki mataki na gaggawa domin kawo karshen maimaita keta tsagaita wutar yaki da ‘yan sahayoniyar suke yi.
Har ila yau, kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce; “ Dalilin da ‘yan sahayoniya su ka bijiro da shi na kai wa Lebanon hari,ba zai zama karbabbe ba, don haka wajibi ne ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki matakin yadda ‘yan sahayoniyar suke keta wutar yaki a cikin Gaza, Lebanon da kuma Syria.
Dr. Baka’i ya bayyana abinda HKI take yi da cewa, baraza ce ga zaman lafiya da sulhu na duniya.
Tun bayan tsagaiwa wutar yaki a kasar Lebanon, HKI tana keta ta a duk lokacin da ta so, kamar kuma yadda ta kafa sansanoni biyar da ta girke sojojinta a ciki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Janar Sari: Sojojinmu Sun Yi Taho Mu Gama Da Amurkawa Sau 3 A Cikin Sa’o’i 24
Kakakin sojan kasar Yemen janar Yahya Sari ya sanar da cewa sau uku su ka yi taho mu gama da sojojin da suke cikin jirgin dakon jirayen yakin Amurka “ Trauman” a cikin sa’oi 24.
A wata sanarwa da janar Yahya Sari ya yi a jiya Asabar ya bayyana cewa; Sun kai wa jirgin dakon jiragen yakin na Amurka da kuma sauran jiragen da suke ba shi kariya a cikin tekun “Red Sea”.
Kakakin sojan na kasar Yemen ya kuma ce; Sun kai wa jiragen na Amuka hare-hare ne da jiragen sama marasa matuki da kuma makamai masu linzami mabanbanta.
An shiga makwanni na uku kenan da sojojin na Yemen suke mayar da martani akan hare-haren da sojojin Amurka da Birtaniya suke kai wa kasarsu.
Kasar ta Yemen tab akin jagororinta za su ci gaba da kai wa manufofin HKI hare-hare har zuwa lokacin da za a daina yaki da Gaza da kuma dauke takunkumin da aka akakaba wa zirin na hana shigar da kayan agaji.
Baya ga kai wa Amurka da Birtaniya da sojojin na Yemen suke yi, suna kuma hana duk wani jirgin ruwa ratsawa ta tekun “Red Sea” matukar zai nufi HKI.
Sa’o’i kadan da su ka gabata ma dai sojojin kasar ta Yemen sun harba makamai masu linzami zuwa HKI