HausaTv:
2025-04-20@23:17:35 GMT

MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu

Published: 29th, March 2025 GMT

Babban sakataren MDD, Antonio Guterres ya yi gargadi a jiya juma’a da safe, akan abinda ya kira ‘yanayi mai  cike da damuwa da yake faruwa a cikin kasar Sudan ta Kudu.

An sami tashin hankali da fadace-fadace a cikin kasar ta Sudan ta kudu a ranar Laraba da jami’an tsaro su ka yi wa mataimakin shugaban kasa na farko Riek Machar daurin talala a cikin gidansa.

Babban magatakardar MDD ya yi kira ga ‘yan siyasar kasar ta Sudan  ta Kudu da su ci gaba da riko da yarjejeniyar sulhu da zaman lafiya,inda ya ce: “ A dawo da gwamnatin hadin kan kasa, da aiki da alkawullan da aka yin a zaman lafiya da sulhu, da hakan ne kadai hanyar dawo da zaman lafiya da kuma yin zabe a cikin watan Disamba 2026.”

A halin da ake ciki a yanzu, kungiyar tarayyar Afirka tana aikin hadin gwiwa da MDD domin kawo karshen  dambaruwar siyasar da ake ciki a kasar.”

Gutrres ya ce; Muna goyon bayan tarayyar Afirka na aikewa da tawagar dattijan nahiyar zuwa Afirka ta kudu da kuma wata tawagar a karkashin jagorancin shugaban kasar Kenya Ruto.

Babban sakataren MDD ya kira yi shugabannin kasar ta Sudan Ta Kudu das u ajiye makamansu na yaki, su kuma bai wa al’ummar kasar fifiko.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo

“Maimakon ya bai wa babban jami’in nasu kudin ya raba wa mutanensa, sai ya zabi rarraba musu shi da kansa”, kamar yadda wata majiya ta shaida wa wannan jarida.

Sai dai, wata majiyar ta shaida wa wakilinmu a ranar Larabar da ta gabata cewa, an gayyaci ‘yansandan ne zuwa babban birnin tarayya Abuja, domin ladabtar da su.

An gayyaci jami’in da sauran yaransa zuwa hedikwatar ‘yansanda da ke Abuja, domin daukar matakan ladabtarwa, in ji majiyar.

Kamar yadda siginal mai dauke da kwanan wata na ranar Talata 15 ga Afrilun 2025, wadda LEADERSHIP ta samu, ya nuna cewa; ‘yansandan da shugaban tawagarsu, DSP Aliyu Adejembi, za su bayyana a hedikwatar ‘yansan da ke Abuja, domin amsa tambayoyi kan rashin da’a da kuma gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • Sojojin Sudan Sun Kashe ‘Yan Tawayen Kasar Ciki Har Da Manyan Kwamandojinsu A Birnin El Fasher
  • Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano
  • Saudiyya da Iran sun jaddada aniyar fadada alakar soji a tsakaninsu