Wike Ya Jinjina Wa Tinubu kan Bunkasa Ilimi Mai Zurfi
Published: 29th, March 2025 GMT
Ya kara da cewa cire Jami’oi daga tsarin albashi na (IPPIS),wanda hakan ne ya ba su Jami’oin tsayawa da kansu kan lamarin da ya shafi ayyukansu wanda har ila yau hakan ya sa ayyukamsu suka kara ingantuwa.
Wike ya yi karin bayani,“akwai maganar amincewa da maganar kudaden bincike na Hukumar TETFund a cikin wasu makarantu, hakan ya kar bunkasa lamarin daya shafi bincike da kirkiro wasu abubuwa.
Su wadannan lamurran na ci gaba sun kara daidaita Jami’oi su maida hankali kan ilimin da suke samarwa domin ya cimma matsalolin da ake fuskanta a karni na ashirin da daya.
da yake bayyana yadda ya ji dangane da karramawar da Hukumar Jami’ar kalaba ta yi masa na ba shi digirin digirgir,Wike ya ce ita karramawar wata girmamawa ce har ila yau,da kuma jan hankalinsa na ya ci gaba da yin ayyukan raya kasa,domin ya jawo hankalin matasa wadanda ke tasowa.
“da na amince da wannan karramawar ina mai farinciki wannan haka nake jin da annashuwa har cikin zuciyata domin zan ci gaba da bayar da gudunmawa sosai kan harkar data shafi ilimi, tafiyar da gwamnati kamar yadda ya dace da kuma ci gaban kasa.
“Ina mai matukar farincikin domin kuwa lamarin ya shiga zuciyata sosai,Jami’ar kalaba ta sa sunana ya cikin tarihin da ake ajiya da zinari,shi yasa ina mai kara yi maku godiya kamar yadda ya jaddada,”.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
“Da farko na ki amincewa saboda hakan ya saba wa tsarin kamfanina, amma bayan na yi tafiyar kusan kilomita biyu sai na ji hakan bai dace ba kuma ‘yan uwana ne daga Jihar Kano, sai na koma na dauke su,” inji direban.
A cewarsa, sun yi tafiya cikin lumana har suka iso Uromi, inda ’yan banga suka tare su. Daga nan ne, shugaban ‘yan bangar ya fara yi wa direban tambayoyi game da kayan da ya dauko da kuma fasinjojin sa. Duk da gabatar da takardar sahalewar hanya amma shugaban ‘yan bangar ya nuna zargi kan mafarautan, musamman saboda makamansu da karnukan da su ke tare da su a cikin motar.
Saboda haka, “Shugaban ‘yan bangar bai amince da su ba ya bukaci su sauko. Da jama’a suka ga irin makamansu da karnuka, sai suka far mana,” in ji direban. “Shugaban ya shaida wa wadanda ke wurin cewa, mu masu garkuwa da mutane ne kuma ‘yan Boko Haram ne, sai suka fara dukanmu.”
Direban tare da wasu mutum biyu, an ce shugaban ‘yan bangar ne ya daure su a hannu tare da kai su ofishin ‘yansanda da ke kusa, inda ya shaida cewa, masu garkuwa da mutane ne ya kamo, lamarin da ya sa aka tsare su cikin gaggawa.
Direban ya bayyana cewa, “A lokacin da aka sake mu na koma wurin, an riga an kashe mutane 16.”
Sai dai ya yi watsi da zargin cewa, lamarin rikicin kabilanci ne. “Wannan ba rikicin kabilanci ba ne, ‘yan banga ne kawai ke da alhakin wannan harin, su ne suka sa aka kashe mutanenmu cikin ruwan sanyi,” in ji shi.
Wannan mummunan lamari dai ya janyo tofin Allah tsine a fadin kasar, tare da yin kira da a gudanar da cikakken bincike domin hukunta wadanda suka aikata wannan aika-aika.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp