Wannan ya sa murnar da wasu ke yi ta komawa da haska finafinan Hausa masu dogon zango a tashar YouTube ta fara komawa ciki.

Me ya sa ba a gamawa din?

BBC Hausa ta ci gaba da cewa wani faifan bidiyo na wata tattaunawa da jagoran shirin Izzar so, Ahmad Lawan ya yi a tasharsa ta Bakori TV, ya ce masu kallo ne ba su gaji da kallon shirin ba, shi ya sa ba zai daina ba.

Ya ce kasancewar Youtube ya dade kudu, amma bai je arewacin Nijeriya ba ne ya sa su ka gwada domin su koya wa mutanen arewa kallon fim a YouTube, shi kuma wannan fim din ya na ciki, ko in ce shi ne daya tilo da ya koya wa mutane kallo a YouTube, kuma mutane ba su gaji da kallonsa ba,” in ji shi, inda ya kara da cewa, “ka ga babu dalilin da zai sa mu daina.”

Na biyu kuma shi ne akwai abubuwa na addini da muke kawowa da suke tasiri a zukatan al’umma kamar soyayyar Annabi SAW, sannan akwai abubuwa da dama da an manta su a cikin addini, idan muka nuna sai su zama matashiya, fitaccen jarumin ya kara da cewa a sanadiyar dim din akwai akalla mutum uku da suka karvi addinin musulunci, wanda a cewarsa hakan na cikin abubuwan da suka sa bai daina fim din ba.

Hakazalika fitaccen marubuci kuma furodusa, Nazir Adam Salihi, wanda yake cikin marubuta shirin dadin kowa mai dogon zango, kuma forudusan shirin Gidan Badamasi, ya ce nan gaba kadan za a fara kammala wasu shirye-shirye.

Ya ce “mu ne muka fara fina-finan nan masu dogon zango, kuma sama da shekara 10 ne da suke wuce ne muka fara zuwa yanzu, a Turai irin su Ingila kuma akwai finafinai masu dogon zango da aka yi shekara 65 ana yi ba a gama ba, ka ga ba za a yi gaggawar cewa ba a gama na Hausa mu da muka fara sama da shekara 10 da suka wuce.”

Sai dai ya ce akwai wasu fina-finai da aka gama daukarsu, “nan gaba kadan zuwa shekara mai zuwa za a kammala wasu fina-finan, a shiga wasu daban, a game da ko ana karancin labaran ne, marubucin ya ce Hausawa na da labarai masu kyau da inganci.

A karshe Salihi ya ba marubuta shawarar su dage da karatu da bincike da kuma natsuwa wajen rubuta labaransu, da yake jawabi kan lamarin, dokta Muhsin Ibrahim, malami a Jami’ar Cologne da ke Jamus ya ce wannan matsala ce ga masana’antar, wadda ba za ta haifa da mai ido ba.

A cewarsa, abin da yake faruwa shi ne masu shirya fina-finan su na fargabar idan suka daina fim din ba dole ba ne wanda za su fara din ya samu karvuwa kamar shi, sai dai ya ce wannan matsala ce babba saboda “babu labarin da ba shi da karshe kuma duk hakurin mai kallo ana iya kure shi.”

Ya ci gaba da cewa duk masana’antun fim na duniya da suka ci gaba a duk labarin da suka tsara, akwai farkonsa da tsakiya da karshe, shi ya sa nake ganin wannan rashin dabara ce saboda yan kallon da suke tunani dai dole sai sun kubuce musu, musamman idan sun samu wani fim da ya fi wannan.

Muhsin ya kara da cewa ya kamata a ce duk wani fim da za a fara, a san cewa za a iya fara wani wanda ya fi shi ko kuma ya gaza shi, misali shirin Labarina mai dogon zango, duk da cewa Aminu Saira ya rike sunan, ai na biyu ya fi na farko karvuwa, shi fim din kamfanin Uk Entertainment ai Garwashi ya fi Fatake karvuwa,” in ji shi.

Ya ce rashin gama fim yana rage wa masu kallo karsashin ci gaba da kallon saboda fargabar ko sun fara kallo, suna tunanin ba za a gama ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano

Shugaban NDLEA, Brig.-Gen. Mohamed Buba Marwa, ya yaba wa jami’an hukumar bisa ƙoƙarinsu wajen yaki da magungunan da kwayoyi na haram, yana mai kira ga al’umma da su ci gaba da bayar da rahoton duk wani abu da ke shafar safarar magunguna.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
  • Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 15 Na Birnin Beijing
  • Amurka ta sanar da cewa za ta rage yawan sojojinta a Syria da rabi
  • Dalilan Da Suke Sa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Ci Gaba Da Tafka Asara A Halin Yanzu
  • Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Har Yanzu Da Akwai Jihohin Da Malaman Makaranta Ke Karbar Albashin Naira 18,000