Aminiya:
2025-03-31@20:08:11 GMT

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki

Published: 29th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kaduna, ta sanar da shirin ɗaukar ma’aikatan lafiya 1,800 aiki don inganta tsarin Kiwon Lafiya a Matakin Farko (PHC) a faɗin jihar.

Wannan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin ma’aikata da kuma inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.

Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Kamar yadda Kwamishiniyar Lafiya, Hajiya Umma Ahmad, ta bayyana, wannan mataki zai taimaka wajen rage yawan mace-macen mata masu juna biyu da yara.

“Wannan mataki zai cike giɓin da ake da shi a cibiyoyin lafiya, domin tabbatar da samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummar Kaduna,” in ji ta.

Gwamnatin jihar ta fara gyara cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 255 tare da samar da kayan aiki na zamani da magunguna.

Wannan zai bayar da damar kula da cututtuka kamar su ciwon suga, hawan jini, da kuma bayar da agajin gaggawa ga mata masu naƙuda.

“Ingantaccen kiwon lafiya ba gata ba ne, haƙƙi ne,” in ji Hajiya Umma, yayin da ta ke jadadda ƙudirin gwamnatin jihar kan kiwon lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Daukar aiki gwamnati Ma aikatan Lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo

Bugu da kari, tawagar za ta gana da shugabannin al’ummar Hausawa na jihar domin tattauna lamarin tare da bayar da shawarwarin da suka dace.

 

Sanarwar ta bukaci ‘yan jihar da su kwantar da hankalinsu tare da kaucewa duk wani abu da zai iya haifar da tarzoma, tare da tabbatar wa jama’a cewa, ana daukar matakan da suka dace na diflomasiyya da na shari’a don magance lamarin yadda ya kamata.

 

Gwamnatin jihar Kano ta mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda lamarin ya shafa tare da yin addu’ar Allah ya jikansu da rahama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Kashe Matafiya: Gwamnatin Kano Ta Aika Tawaga Zuwa Edo
  • Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 
  • Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
  • Jami’an Tsaro A Jihar Kano Na Tarayyar Najeriya Sun Hana Bikin Dabar NA Sallar Bana
  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jadadda Kudurin Ta Wajen Samarda Tsaftatacen Ruwan Sha Ga Al’umma