Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Published: 29th, March 2025 GMT
Wannan hanya, na matukar taimakawa sosai wajen sarrafa sinadarin insulin a jikin mutum.
2-Maganin Hawan Jini (Hypertension)
Ganyen mangwaro na rage matsin jini, sannan kuma yana karfafa jijiyoyin jini.
Saboda haka, a nan sai a nemi sabbin ganyen mangwaro, a tafasa su sosai a tace, sannan a sha rabin kofi da safe da kuma yamma.
3-Maganin Basir Sadidan
Idan ana fama da basir, za a iya amfani da ganyen mangwaro don rage kumburi da ciwo.
Bayan an samu wannan ganye na mangwaro, sai a busar da shi a kuma daka shi har sai ya zama gari. kana sai a dauki cokali daya na garin a hada da rabin kofi na ruwan dumi, sannan a zuba zuma a ciki kadan a sha kullum har sai an samu sauki.
4-Maganin Cututtukan da ke Cikin Baki
Idan ana fama da kuraje a baki, zubar jini daga hakora ko kuraje a harshe, ganyen mangoro na da matukar amfani wajen magance su.
A nan, tafasa ganyen za a yi a tace, sannan a yi amfani da ruwan wajen wanke baki sau uku a rana. Idan ana so kuma za a iya kara gishiri dan kadan, don karin karfi.
5-Maganin kunar Wuta
Idan aka samu kuna, ganyen mangoro na taimakawa wajen rage radadi da saurin warkewa.
Saboda haka, sai a busar da ganyen, a kone shi har sai ya zama toka. Sai a yi amfani da tokar wajen shafawa a wurin da aka konen.
6-Maganin Cututtukan da Suka Shafi Ciki
Ganyen mangwaro na taimakawa wajen magance matsalolin ciki, kamar ciwon ciki da kuma gudawa.
A nan za a tafasa ganyen ne, sannan a rika shan ruwan kullum sannu a hankali.
7-Rage Zafin Jiki da Rashin Nutsuwa (Stress & Andiety)
Idan ana fama da zafin jiki ko rashin hutu, ganyen mangwaro na taimakawa kwarai da gaske wajen kawar da su.
Za a tafasa shi, sannan a rika shan ruwan ko kuma a rika yin wanka da shi, domin samun nutsuwa.
8-Maganin Cututtukan Huhu (Tari, Mura da Sanyi)
Ganyen mangwaro na taimakawa wajen maganin tari, mura da kuma sanyi.
Ana tafasa shi a sha ruwan, domin rage tari da samun waraka daga cutar mura da kuma ta sanyi.
9-Inganta Lafiyar Mahaifa da Haihuwa
Ganyen mangwaro na da matukar amfani ga mata masu fama da matsalolin mahaifa.
Har ila yau, yana taimakawa wajen tsaftace mahaifa da kuma kara samun damar haihuwa.
don haka, a nan sai a tafasa ganyen a tace shi, sannan a rika shan sa da dumi.
10-Maganin Makakin Makogwaro da Ciwon Wuya
Idan ana fama da kuraje a makogwaro ko ciwon wuya ko kuma makaki, ganyen mangwaro na taimakawa kwarai da gaske wajen warkar da su.
Saboda haka, sai a tafasa shi sosai a yi amfani da ruwan ta hanyar kurkurawa da safe da kuma yamma.
Bugu da kari, ganyen mangwaro na da matukar amfani ga lafiyar jikin dan’adam. Idan ana son cin gajiyar fa’idarsa yadda ya kamata, yana da kyau a rika amfani da shi akai-akai.
Sannan, duk da haka; yana da matukar kyau a nemi shawarar likita kafin
a fara amfani da kowane irin maganin gargajiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Mangwaro Sirri ganyen mangwaro na taimakawa Ganyen mangwaro na taimakawa na taimakawa wajen na da matukar
এছাড়াও পড়ুন:
Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi
Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya musanta cewa akwai tsamin dangantaka tsakaninsa da Gwamnatin Sakkwato.
Ana iya tuna cewa bayan karɓar akalar jagoranci ne Gwamna Ahmed Aliyu ya yi wa Dokar Masarautar Sakkwato gyaran fuska tare da sauke wasu sarakunan gargajiya, lamarin da aka riƙa raɗe-raɗin wani yunƙuri ne tsige shi kansa Sarkin Musulmin.
Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wutaSai dai da yake jawabi a saƙonsa na barka da sallah, Sarkin Musulmi ya ce “ba wata rashin jituwa ko faɗa a tsakaninmu.
“Muna aiki tare a koyaushe. Aikinmu mu taimaka wa gwamnatin [Sakkwato] kan shirye-shiryen da ta ɗauko domin ciyar da jama’a gaba.”
Ya yi kira ga al’ummar musulmi da su ci gaba da yi wa shugabanni addu’a domin samun nasara wajen sauke nauyin jama’a da rataya a wuyansu.
Kazalika, Alhaji Sa’ad ya ce karantarwar addini da aka samu a watan Azumi mai albarka abu ne da ya kamata a riƙe a sanya cikin aiki.
“Mu ƙara ɗaure ɗamara kar mu koma gidan jiya wajen aikata saɓon Allah. Mu dage da yin ibada kar a ja baya. Sannan mu riƙa yi wa shugabanni addu’a.
“Ku kuma shugabanni ku ji tsoron Allah cikin jagoranci. Idan za a yi ayyukan jama’a kar a ji tsoron kowa sai Allah,” in ji Sarkin Musulmi.
Sarkin ya yi kira ga jami’an tsaro da su ktara ƙaimi wajen magance matsalar tsaro domin a cewarsa har yanzu akwai sauran aiki a ba iya Jigar Sakkwato kaɗai ba.