HausaTv:
2025-03-31@20:00:42 GMT

Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya

Published: 29th, March 2025 GMT

Wani babban mai bawa jagoran juyin juya halin musulunci Imam Ayatullahi Sayyid Aliyul Khaminae shawara kan harkokin tsaro ya bayyana cewa hare-haren ‘WaaduSsadik na III’ don maida martani kan HKI saboda hare-haren da ta kaiwa Iran a shekarar da ta gabata suna kan hanya.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Manjo Janar Yahya Rahim Safavi yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa, Tehran tana kan bakanta na maida martani kan HKI saboda hare-haren da ta kai kan wasu wurare a nan Iran daga cikin har da wani barikin sojoji a nan birnin Tehran a shekarar da ta gabata.

Safari ya kara da cewa, jinkirin da aka samu na maida-martani yana da hikima a cikinsa. Sannan karfin maida martanin sai ya nininka wadanta ta kai a wa’adussadik na II.

Ya kuma kara da cewa shugabanci a JMI yana da wayo, da dogon tunani da kuma tsari mai kyau.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora : A yau, duniyar musulmi tana bukatar hadin kai

Jagoran juyin juya halin musulinci na Iran,Ayatullah Sayyid Ali Khamenei, ya bayyana cewa yau duniyar musulmi tana bukatar hadin kai fiye da ko wane lokaci.

A yayin ganawarsa da jami’an tsare-tsare da jakadun kasashen musulmi yau Litinin ranar karamar sallah a Iran, Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya mayar da hankali kan abubuwan da ke faruwa a yankin inda ya ce a yau wani bangare na duniyar musulmi ya samu munanan rauni.

‘’ Falasdinu ta ji rauni, Lebanon ma ta ji rauni,  inji shi. Laifukan da aka aikata a wannan yanki ba a taba ganin irinsa ba, an kashe yara kusan 20,000.”

Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bukaci a hankali tare da daukar nauyin da ya rataya a kan wannan lamari.

“A yau, hakika duniyar musulmi tana bukatar hadin kai inji jagoran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari
  • Jagora : A yau, duniyar musulmi tana bukatar hadin kai
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Jakadan Kasar Rasha A Saliyu Ya Ce Kasar Rasha Tana Nazarin Yiyuwar Fara Hakar Ma’adinin bauxite A Kasar
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza
  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • Maduro Ya Bayyana Sakataren Harkokin Wajen Amurka Da Cewa Wawa Ne