HausaTv:
2025-04-20@23:20:20 GMT

Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya

Published: 29th, March 2025 GMT

Wani babban mai bawa jagoran juyin juya halin musulunci Imam Ayatullahi Sayyid Aliyul Khaminae shawara kan harkokin tsaro ya bayyana cewa hare-haren ‘WaaduSsadik na III’ don maida martani kan HKI saboda hare-haren da ta kaiwa Iran a shekarar da ta gabata suna kan hanya.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Manjo Janar Yahya Rahim Safavi yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa, Tehran tana kan bakanta na maida martani kan HKI saboda hare-haren da ta kai kan wasu wurare a nan Iran daga cikin har da wani barikin sojoji a nan birnin Tehran a shekarar da ta gabata.

Safari ya kara da cewa, jinkirin da aka samu na maida-martani yana da hikima a cikinsa. Sannan karfin maida martanin sai ya nininka wadanta ta kai a wa’adussadik na II.

Ya kuma kara da cewa shugabanci a JMI yana da wayo, da dogon tunani da kuma tsari mai kyau.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kaddamar Da Sabbin Hare-Hare Kan Garuruwan Sana’a, Sa’adah Da Al-Jawf Na Kasar Yemen

Kasar Yemen ta sanar da cewa: Amurka ta kaddamar da sabbin hare-haren wuce gona da iri kan garuruwan Sana’a, Sa’dah, da Al-Jawf

Mahukuntan Yemen sun sanar da cewa: Amurka ta ci gaba da kai hare-hare kan kasar Yemen, inda ta kaddamar da wasu jerin hare-hare kan garuruwan Sana’a, Sa’dah da Al-Jawf.

Wakilin Al-Alam ya ruwaito a yammacin jiya Juma’a cewa: Jiragen saman yakin Amurka sun kaddamar da hare-hare har sau shida a gundumar Bani Hushaysh dake arewa maso gabashin birnin Sana’a fadar mulkin kasar Yemen, inda suka yi luguden wuta a wurare da dama.

A lardin Al-Jawf, an kai wasu hare-hare 4 ta sama a gundumar Bart Al Anan da yankin Al-Yatmah da ke gundumar Khab da gundumar Al Sha’af a arewa maso gabashin kasar Yemen.

A ranar alhamis din da ta gabata, rundunar kawancen da Amurka ke jagoranta ta kaddamar da hare-haren wuce gona da iri kan birnin Al-Hodeida, inda suka yi ta kisan kiyashi kan fararen hula da ma’aikata a tashar Ra’as Issa da ke birnin. Hare-hare 14 ne suka kai kan cibiyoyin tashar jiragen ruwa da tankunan mai da iskar gas, inda suka kashe fararen hula fiye da 80 tare da raunata wasu 160, bisa ga kididdigar farko, a cewar ma’aikatar lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Bayyana Cikakken Ikon Tawagar Masu Tattaunawan Iran A Zaman Shawarwari Da Amurka
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Amurka Ta Kaddamar Da Sabbin Hare-Hare Kan Garuruwan Sana’a, Sa’adah Da Al-Jawf Na Kasar Yemen
  • Dakarun Gwagwarmayar Yemen Sun Kai Hare-Haren Daukan Fansa Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna Alia
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun
  • Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da  Saudiyya