Kungiyar JIBWIS a Karamar Hukumar Giwa ta bukaci al’ummar Yakawada da su ci gaba da rungumar koyarwar Al-Qur’ani a rayuwarsu ta yau da kullum.

Mataimakin Shugaban kungiyar, Malam Ibrahim Mustafa Shatiman Giwa, ya yi wannan kira ne yayin bikin rufe Tafsirin Ramadan na bana da aka gudanar a Masallacin JIBWIS da ke Yakawada.

Malam Ibrahim Mustafa ya bayyana jin daɗinsa kan goyon baya da jajircewar al’ummar Yakawada a duk tsawon Tafsirin. Ya jaddada muhimmancin kiyaye darussan da aka koya a cikin Ramadan tare da amfani da su a rayuwa bayan karewar watan mai alfarma.

A nasa jawabin, Sheikh Suleman Abdulkarim Fatika ya nuna godiyarsa ga dukkan mahalarta Tafsirin da suka daure suka halarta tun daga farkon watan Ramadan har zuwa karshensa.

Ya yaba da sadaukarwarsu tare da ƙarfafa su da su ci gaba da neman ilimi da fahimtar addini.

Taron rufe Tafsirin Ramadan din ya samu halartar malamai, shugabannin al’umma, da musulmi mabambanta, wanda hakan ya jaddada mahimmancin koyarwar addini wajen haɓaka haɗin kai da kyawawan ɗabi’u a cikin al’umma.

COV/Magaji Yakawada

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: 2025 Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

An Ga Watan Sallah A Ƙasar Saudiyya

Hukumomin a Ƙasar Saudiyya, sun tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal, wanda ke nuna ƙarshen azumin watan Ramadan na bana.

Kwamitin duban wata na ƙasar ya bayyana cewa an ga jinjirin wata a yammacin yau, wanda ke tabbatar da cewa gobe za a fara bukukuwan Sallah.

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah Abubuwan da Za ki Runguma domin Burge Mijinki

Wannan na nufin cewa al’ummar Musulmi a Saudiyya za su yi bikin ƙaramar Sallah, domin kammala azumin da suka gudanar a tsawon watan Ramadan.

Hukumomi sun buƙaci jama’a da su gudanar da bukukuwan Sallah cikin lumana da bin dokoki don tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
  • Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • Gobe Ta Ke Sallah A Nijeriya – Sarkin Musulmi
  • An Tabbatar Da Ganin Watan Shawwal A Nijeriya
  • An Ga Watan Sallah A Ƙasar Saudiyya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]