Gwamnati Ta Ba da Umarnin Tafiya Yi Wa Ƙasa Hidima Ga Duk Masu HND
Published: 29th, March 2025 GMT
Yawancin wadanda suke da HNd basu samu damar tafiya aikin Yiwa kasa Hidima/Aikin Bautawa kasa wanda hakan ne kuma aka gay a kamata ayi masu adalci kan lamarin
Sai dai kuma irin ci gaban da aka samu ya kawo ko samar da wata matsala ta yadda wadanda suka yi karatun suka kammala a makaranta sai ta kasance wasu daga cikinsu basu samu damar tafiya aikinyiwa kasa hidima ba saboda irin karatun da suka yi.
Da yake bada ta shi gudunmawa darekatan lamurran ‘yan jaridu da hulda da jama’a ma’aikatar ilimi ta tarayya Boriowo Folasade, ya fitar da sanarwa wadda take tabbatar da gaskiyar lamarin na abubuwan da suka biyo bayan dukkan tarurrrukan da kuma ganawar da aka yi.
Sanarwa ta nuna cewa sabon matakin da aka dauka wani abin farincikine ga wadanda suka kammala karatun da ake samun Babbar difiloma ta kasa HNd wadanda a baya ba a basu damar tafiya wuararen da za su yiwa kasa hidima ba.
An ma bayyana cewar matakan da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta dauka na tabbatar da cewar ana yin adalci ya kasance ana tafiya da kowa a lamarin ilimi na Nijeriya.
Su ma wadanda suka kammala karatun nasu ba irin na wadanda suka zauna a makaranta ba, suma za su iya je aikin yiwa kasa hidima na shekara daya da takwarorin su wadanda suka samu ko karatun da ya basu damar samun digiri suke yi.
Domin samu daukar mataki wanda ba’a vata lokaci ba an umarci Hukumar kula da ilimin daya shafi fasaha da kere- kere (NBTE)ta gaggauta samar da bayanai na wadanda suka kammala HNd domin tafiya harkar ta yi wa kasa hidama NYSC.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
Nijar ta fice daga rundunar tsaro ta haɗin gwiwa da ke yaƙi da masu iƙirarin jihadi a Tafkin Chadi da ke yammacin Afirka yayin da take ƙoƙarin inganta tsaro kan albarkatun mai a cikin gida.
A shekarar 2015 ce Nijeriya da Chadi da Kamaru da Nijar suka sake farfaɗo da rundunar haɗin gwiwa ta Multinational Joint Task Force (MNJTF), wacce aka ƙirƙira a shekarar 1994 don yaƙi da ƙungiyoyin jihadi a kewayen Tafkin Chadi.
NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana Azumin Sitta Shawwal a MusulunciSai dai har yanzu ana ci gaba samun rarrabuwar kai da matsalar rashin daidaito na hana rundunar samun nasara sosai, lamarin da ya sa ƙungiyoyin ‘yan bindiga a yankin cin karensu ba babbaka.
Kamfanin Dillancin Labaran Reuters da ya ruwaito sanarwar gwamnatin ƙasar Nijar ɗin ya ce kawo yanzu MNJTF ba ta yi tsokaci game da ficewar Nijar ɗin ba, yana mai ƙarawa da cewa babu tabbas game da yadda matakin zai yi tasiri kan aikin rundunar a nan gaba.
Yankin Tafkin Chadi yana fama da hare-haren ‘yan bindiga ciki har da ‘yan kungiyar ISWAP da Boko Haram, waɗanda suka ƙaddamar da yaƙi a arewa maso gabashin Nijeriya a shekarar 2009 kuma sun kashe dubban mutane.
A bara, Chadi ta yi barazanar ficewa daga MNJTF bayan an kashe sojojinta kusan 40 a wani harin da aka kai wani sansanin soji.
Nijar tana rage hulɗa da wasu maƙwabtanta tun bayan da sojoji suka hamɓarar da gwamantin Shugaba Mohamed Bazoum a shekarar 2023. Tare da Burkina Faso da Mali – ƙasashe maƙwabta, inda sojoji suka karɓe kwanan nan – ta janye daga ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS) a shekarar 2024.
Sojojin da ke mulki a Nijar, da suka yi shelar tsarin miƙa mulki na shekara biyar, sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a ƙasar, wadda ‘yan ci-rani da masu safarar mutane ke ƙetarewa ta cikin gagarumar hamadar arewacinta.