Leadership News Hausa:
2025-04-21@06:32:01 GMT

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

Published: 29th, March 2025 GMT

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

A shekarar 1468 wanda yake mulkin Sonni Ali Shugaban Songhai ya ci wurin da yaki.Shi ba wanda yake ya saki jikinsa bane musamman ma musulmai wadanda suke da ilimin musulunci,amma wanda ya gaje shi Askia Muhammad na daya (1) wanda ya yi mulkin kasar daga shekarar( zuwa 1493–1528)ya yi amfani ne da wadanda suka yi karatu a matsayin wadanda yake tuntuva dangane da abinda ya shafi shari’a da al’amura na yau da kullum.

Bayan da kasar Morocco ta mamaye ta a shekarar 1591, daga nan sai Birnin ya fara komawa baya.Aka bada umarni na kama Malamanta a shekarar 1593 saboda ana yi masu kallon basu goyon bayan abinda aka yi; an kashe wasu daga cikinsu lokacin da aka yi wani gumurzu, yayin da wasu kuma aka tura su gudun hijira zuwa Morocco.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tarihi

এছাড়াও পড়ুন:

Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP

Jam’iyyar adawa ta SDP buƙaci Shugaba Bola Tinubu da sauran shugabannin siyasa a Najeriya su dai shagala da batun zaɓen 2027, su mayar da hankalinsu wajen magance matsalar tsaro da ke ƙara mayar da ƙasar tamkar filin kisa.

SDP ta bayyana cewa kashe-kashe ɗaruruwan mutane da ke faruwa a faɗin ƙasar nan – Arewa da Kudu – musamman a makonnin da suka gabata, na da matuƙar tayar da hankali.

Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na SDP, Araba Rufus Aiyenigba, ya bayyana a wata sanarwa da ya fitar a daren Juma’a, cewa abubuwan takaicin sun hada da da kisan mafarautan Jihar Kano a jihar Delta, baya ga ayyukan ’yan ta’adda da hare-haren da a ka yi wa mutane sama da 100 a sassan jihar Filato.

Ya ce gwamnatin da ke kan mulki a yau ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita da za ta dakatar da wannan zubar da jini da ke gudana, yayin da ƙasar nan ke saurin zama filin kisa.

Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo

“A wasu makonnin da suka gabata, an kai munanan hare-hare da kisan gilla da ƙona wasu maharba daga Jihar Kano a yankin Edo, a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa arewa daga wani farauta a yankin Neja Delta.

“Haka kuma, a makon da ya gabata, an kashe sama da mutane ɗari ta hanyar kisan gilla tare da ƙona gidaje da yawa a Filato!

“An kuma ruwaito cewa wata sabuwar ƙungiyar ta’addanci mai suna ‘Makmuda’ ta kashe mutane da yawa, wanda ya ƙara dagula al’amuran ƙasarmu,” in ji Aiyenigba.

Ya yi zargin cewa jami’an tsaron ƙasar nan suna ƙara kasala da rashin ƙarfi, yayin da gwamnatin da ke kan mulki ta rasa duk wata dabara mai ma’ana kuma ta kasa samar da wata mafita.

Ya ce, “Abin damuwa ne yadda duk waɗannan kashe-kashe da ɓarna ke faruwa ba tare da an yi wani abu ba.

“’Yan siyasa a bayyane yake cewa, sun fi damuwa ne kawai da batun zaɓen 2027 da ke tafe. Muna buƙatar yin aiki don tabbatar da tsaron masu zaɓe kuma mu mallaki ƙasa kafin ma a fara maganar zaɓe,” in ji shi.

Kakakin jam’iyyar SDP na ƙasa ya ce yanzu ne lokacin da Tinubu zai nuna ƙarfin hali da ƙarfin zuciya a matsayinsa na shugaba, ya kuma yi abin da ya dace don tabbatar da tsaron al’ummar Najeriya.

“A matsayinsa na shugaban ƙasa, wajibi ne ya tabbatar da tsaron ’yan ƙasa, kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada, cewa jin daɗin jama’a da tsaro su ne babban manufar gwamnati.”

Ya ci gaba da mika ta’aziyyar jam’iyyar bisa rashe-rashen da aka yi a sakamakon wadannan matsalolin tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunoni 9 Sun Tsere Daga Gidan Gyara Hali A Jihar Kwara, An Cafko Guda Daya
  • Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari?
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
  • Ana kashe ’yan Najeriya amma Tinubu ya fi damuwa da Zaɓen 2027 — SDP
  • Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.