Aminiya:
2025-04-21@06:34:53 GMT

Rikici ya ɓarke bayan wata mata ta mari ɗan sanda a Saudiyya

Published: 29th, March 2025 GMT

Hukumar ’Yan Sandan Saudiyya, ta yi magana kan bidiyon da ke yawo a shafukan sada zumunta, wanda ya nuna wata mata tana mari wani ɗan sanda bayan ya hana ta wuce wata hanya da aka rufe.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Asabar, ta ce tana bincike domin tattara dukkanin bayanai kafin ɗaukar matakin da ya dace bisa doka.

Girgizar ƙasa ta hallaka sama da mutum 1000 a Myanmar Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo

Bidiyon, wanda ya bayyana a ranar Juma’a, ya nuna matar tare da wata ƙawarta suna tunkarar wajen da aka kange, inda jami’an tsaro suka hana su wucewa.

Sai dai matar ta fusata, tare da marin ɗan sandan, shi ma daga bisani ya rama kafin wasu su shiga tsakani.

Lamarin ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta, inda mutane da dama ke ganin matar ta ci zarafin jami’in tsaron yayin da yake bakin aikinsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: askar Ɗan Sanda mari Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Rahoton Hana Shettima Shiga Villa

Fadar Shugaban Ƙasa ta buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da irin waɗannan labaran ƙarya, tare da kira ga kafafen yaɗa labarai su riƙa tabbatar da gaskiya labari kafin wallafawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ango ya tsere tare da surukarsa
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Rahoton Hana Shettima Shiga Villa
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja
  • Dole Kwankwaso Ya Nemi Afuwarmu Kafin Ya Komo APC
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Iran Da Saudiyya Za Su Iya Magance Yawancin Matsalolin Yankin Gabas Ta Tsakiya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun