Aminiya:
2025-04-02@03:08:07 GMT

Rikici ya ɓarke bayan wata mata ta mari ɗan sanda a Saudiyya

Published: 29th, March 2025 GMT

Hukumar ’Yan Sandan Saudiyya, ta yi magana kan bidiyon da ke yawo a shafukan sada zumunta, wanda ya nuna wata mata tana mari wani ɗan sanda bayan ya hana ta wuce wata hanya da aka rufe.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar Asabar, ta ce tana bincike domin tattara dukkanin bayanai kafin ɗaukar matakin da ya dace bisa doka.

Girgizar ƙasa ta hallaka sama da mutum 1000 a Myanmar Mutum 14 sun shiga hannu kan kisan ’yan Arewa a Edo

Bidiyon, wanda ya bayyana a ranar Juma’a, ya nuna matar tare da wata ƙawarta suna tunkarar wajen da aka kange, inda jami’an tsaro suka hana su wucewa.

Sai dai matar ta fusata, tare da marin ɗan sandan, shi ma daga bisani ya rama kafin wasu su shiga tsakani.

Lamarin ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta, inda mutane da dama ke ganin matar ta ci zarafin jami’in tsaron yayin da yake bakin aikinsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: askar Ɗan Sanda mari Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Habaka Jama’ar Kano

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, a ranar Talata ya yaba wa Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano bisa bayar da fifiko akan ilimi, kiwon lafiya, noma, da tsaro a jihar. Sarki Sanusi II ya bayyana jin dadinsa ne a lokacin da ya kai gaisuwar Sallah ga gwamnan Kano, kamar yadda aka saba gudanarwa a al’adance duk shekara. Sin Da Zambiya Sun Daddale Yarjejeniyar Fitar Da Kwarurun Macadamia Nuts Farashin Man Fetur Ya Ƙara Tashi Sakamakon Rikicin Dangote Da NNPCL “Mun zo ne domin mika gaisuwar mu ta barka da Sallah tare da gode muku bisa gagarumin aikin da kuke yi, musamman a fannin ilimi da noma, inda kuka samar da tallafin kayan aikin noma na zamani. “Muna godiya ga Allah da ya ba mu damar shaida wannan lokaci na musamman, inda muke taruwa don sake gaishe da Gwamna a yayin bikin Sallah,” in ji shi. Sanusi ya yabawa ‘yan majalisar dokokin jihar Kano bisa bin doka da oda da suka yi, wanda ya ce ya dawo da tsari da kimar masarautar. “Muna fatan gwamnan zai ci gaba da yin aiki mai kyau, kuma muna kira ga shugabannin kananan hukumomin da su yi koyi da shi, su kara kaimi,” in ji Sarkin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Habaka Jama’ar Kano
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi
  • Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Abubuwan da ya kamata Musulmi ya yi a ranar Karamar Sallah