Majalisar Karamar Hukumar Jahun dake Jihar Jigawa ta kaddamar da rabon tallafin kayan noman rani ga manoma 300.

 

A jawabinsa wajen bikin da aka gudanar a Garin Darai, shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam yace hakan na daga cikin manufofin Gwamna Umar Namadi na bunkasa noman rani da na damina domin kawar da yunwa da kuma samar da abinci ga al’umma.

A cewar sa, karamar Hukumar ta ware wasu yankunan Sahara domin fara noman rani a karo na farko dan fadada harkar noma a kan Tudu.

 

Alhaji Jamilu Danmalam yace an zabi kauyen Tunubu dake mazabar Kanwa domin fara noman Rani.

Ya kara da cewar, wadanda suka anfana da tallafin za su ci moriyar kaso 60 cikin 100, yayin da zasu dawowa da gwamnati kaso arba’in kacal 40.

 

A nasa jawabin, jami’in kula da noman rani Malam Suraja Dahiru ya ce gwamnatin Jihar Jigawa ta bada umarnin baiwa matasa filin noma a kalla kadada 100 a kowacce karamar hukuma.

Ya yi nuni da cewar, shugaban karamar Hukumar Jahun ne kadai ya kara adadin filin noma zuwa dari uku.

 

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, kayayyakin tallafin da aka raba sun hada da Injin ban ruwa da takin zamani buhu bakwai da irin shuka na shinkafa buhu daya da injin feshi da maganin kwari da sauran kayan aikin gona.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Jahun Noman Rani

এছাড়াও পড়ুন:

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

Shugaban ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a fannin cewa, ako da yaushe, kofar Hukumar ta NPA, bode take domin hadaka wacce ta zarce ta gudanar da baje koli.

Dakta Dantsoho ya kara da cewa, an samar da tsarin na EPT domin a tabbatar da cewa, ana fitar da kaya zuwa waje, ta hanyar yin amfani da na’urar zamani.

“Wannan na zai taimaka matuka wajen kaucewa samun jinkiri da kuma mai-maita aiki da Hukumar ta saba fuskanta a baya,” A cewar Dantsoho.

Kazalika, Dantsoho ya bayyana cewa, domin a samu sauki wajen kai kaya a tsakanin masu kananan da matsakaitan sana’oi, musamman duba da cewa, tsarin na EPT, zai taimaka matuka ga guraren da ake adana kaya a cikin kasar na, da kuma hada karfi da karfe da Hukumar Bunkasa Harkokin Fitar da Kayayyaki ta Kasa NEPC da sauran abokan hadaka.

“Domin Hukumar ta NPA ta gudnar da ayyukanta daidai da tsarin Gwamnatin Tarayya na samar da sauki ga yin kasuwanci, musamman duba da taken baje kolin na ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, Hukumar NPA ta samar da tsarin samar da sauki wajen bai wa ‘yan kasuwar kasar yadda za su rinka fitar da kayansu, zuwa ketare,”. Inji Dantsoho.

Shugaban ya kara da cewa, Hukumar ta kuma nasara a tsarinta na NSW, musamman duba da yadda aka samu saduwa da sauran masu ruwa da tsaki, wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci

Dantsoho ya jinjinawa mahukunta Cibiyar ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, musamman kan yadda suke ci gaba da gudanar da hada-hara kasuwanci da yanyo abokan kasuwanci na cikin gida Nijeriya, da kuma na kasashen waje, wanda hakan ya kara taimakawa, wajen habaka tattalin arzikin kasar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, duba da yadda jihar ta Enugu ta kasance a yankin Kudu Maso Gabas, hakan zai taimaka mata wajen samar da damar kara fadada fitar da kaya zuwa ketare.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • Ruftawar gini ta kashe mutum 5 a Legas
  • Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe
  • Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
  • Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare
  • Sarakuna Suna Bada Gudunmuwa Wajen Samarda Lafiya Da Hadin Kan Kasa– Kungiyar Sarakunan Afirka
  • Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista