HausaTv:
2025-04-21@11:16:01 GMT

Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644

Published: 29th, March 2025 GMT

Hukumomi a Myanmar sun ce adadin wadanda suka mutu a girgizar kasar ya kai 1,644, yayin da wasu 3,408 suka jikkata, ye zuwa ranar Asabar din nan.

Tunda farko dai mutane 1,007 ne aka sanar sun mutu sai wasu 2,389 da suka jikkata.

Girgizar mai karfi maki 7.7 ta shafi Kasashen Myanmar da Thailand wadanda suk suka ayyana dokar ta baci a ranar Juma’a.

Tuni kasar Myanmar ta nemi taimakon kasashen duniya da kuma kungiyoyi don agazawa wadanda girgizar kasarta shafa.

Kasar Iran ta ce a shirye take ta taimakawa kasashen biyu da girgizar kasar ta shafa.

A wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ya fitar yau Asabar ya ce Iran a shirye take ta shiga ayyukan agaji da ceto a kasashen biyu.

Baghai ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa da kuma gwamnatoci da al’ummomin kasashen biyu.

Ayyukan agaji na kasa da kasa sun fara kwararowa cikin kasar: masu aikin ceto da agaji da suka hada da barguna, kayan abinci da na bincike, daga kasashen China da Indiya da ke makwabtaka da su, da kuma wasu kasashe.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a girgizar kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Fursunoni 9 Sun Tsere Daga Gidan Gyara Hali A Jihar Kwara, An Cafko Guda Daya

An samu rahoton cewa, Fursunoni tara a gidan yari na Oko Erin a jihar Kwara a ranar 19 ga watan Afrilu, sun tsere. Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zagazola Makama cewa, da misalin karfe 10:00 na dare, wani ma’aikaci a gidan, mai suna Joseph Issa, ya sanar da faruwar lamarin. Rugujewar Gini A Legas: Adadin wadanda Suka Mutu Ya Kai Biyar, An Ceto 20 Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia Ba tare da bata lokaci ba, ‘yansanda suka yi gaggawar isa wurin, inda suka sake kama daya daga cikin wadanda suka tsere, mai suna Abdul Raman Misa mai shekaru 15. An mayar da Misa gidan yarin, yayin da ake ci gaba da neman sauran takwas din da suka arce. A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da bincike kan yadda suka tsere.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Fursunoni 9 Sun Tsere Daga Gidan Gyara Hali A Jihar Kwara, An Cafko Guda Daya
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Rugujewar Gini A Legas: Adadin wadanda Suka Mutu Ya Kai Biyar, An Ceto 20
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yaba Da Zaman Tattaunawan Iran Da Amurka Zagaye Na Biyu A Birnin Roma
  • Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • An kashe sojoji, fararen hula da dama a Borno