Siriya : Ofishin jakadancin Amurka ya yi gargadi game da yiyuwar hare-hare a yayin bikin sallah
Published: 29th, March 2025 GMT
Ofishin jakadancin Amurka da ke Damascus ya fitar da wata sanarwar gaggawa, inda ya yi kira ga daukacin Amurkawa da su gaggauta ficewa daga kasar Syria, sakamakon karuwar hare-haren da ake kai wa a lokacin bukukuwan sallar Idi, wanda ke kawo karshen azumin watan Ramadan mai alfarma.
A cikin wata sanarwa da ta fitar ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta daukaka tafiye-tafiye zuwa Syria zuwa mataki na 4 mafi girman inda aka gargadi, Amurkawa da kada su je kasar Siriya bisa kowane dalili.
Ofishin jakadancin ya gargadi ‘yan kasar game da yiwuwar kai hari kan “ofisoshin jakadanci, kungiyoyin kasa da kasa da cibiyoyin jama’a na Syria” a Damascus.
Halin tsaro a Syria ya tabarbare bayan da kungiyoyin ‘yan ta’adda, karkashin jagorancin Hay’at Tahrir al-Sham, suka hambarar da gwamnatin Bashar al-Assad a ranar 8 ga Disamba, 2024.
Tun bayan rugujewar gwamnatin Assad, sojojin Isra’ila ke kai hare-hare ta sama a kan cibiyoyin soji, da kuma rumbun adana kayan yaki na sojojin Siriya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
Hukumomi a jihar Benue dake Najeriya sun ce adadin wadanda suka mutu a harin da ‘yan bindiga suka kai a hukumomin Ukum da Kogo ya kai 56.
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, a wata ziyara a yankin ya shaidawa manema labarai cewa adadin wadanda suka mutu a harin ya kai 56.
”A yanzu, mutum 56 ne suka mutu wadanda ba su ji ba su gani ba, da suka hada da iyaye da maza da mata da kananan yara”, in ji shi.
Gwamnan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gaggauta daukar matakai domin kawo karshen hare-hare a jihar.
Gwamnan ya ce tuni gwamnatin jihar ta kara tura jami’an tsaro zuwa yankunan domin kwantar da hankula.
Harin na zuwa ne kimanin mako biyu bayan wasu yan bindiga sun kashe fiye da mutum 100 a wasu hare-hare a jihar Plateau mai makwabtaka.