Aminiya:
2025-05-07@03:06:59 GMT

Gobe take Sallah a Nijeriya — Sarkin Musulmi

Published: 30th, March 2025 GMT

An ga jinjirin watan Shawwal a Nijeriya da ke tabbatar da ƙarewar watan azumi na Ramadanan bana.

Ɗaya daga cikin ’yan kwamitin duban wata a Nijeriya (NMSC), Malam Simwal Usman Jibrin ne ya sanar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Sai dai ya ce ana dakon sanar da ganin jinjirin watan a hukumance daga Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Islama a Nijeriya da ke ƙarƙashin jagorancin mai alfarma Sarkin Musulmi.

Hakan ya tabbatar da ƙarewar watan azumi na Ramadanan bana, saboda haka gobe Lahadi take Sallah a Nijeriya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya Ramadan Shawwal

এছাড়াও পড়ুন:

Iran da Saudiyya sun jaddada bukatar kare hurimin kasar Siriya

Kasashen Iran da kuma Saudiyya sun jaddada kiran su na ganin an kare hurumin kasar Siriya tare kuma da yin tir da hare-haren da Isra’ila ke kai wa kasar.

Jami’an Iran da Saudiyya sun tabbatar da aniyarsu ta tabbatar da ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Siriya, tare da yin Allah wadai da harin da sojojin Isra’ila suka kai kan al’ummar kasar Larabawar.

An bayyana hakan ne a wata ganawa da aka yi a ranar Lahadi a birnin Riyadh tsakanin Mohammad-Reza Raouf Sheibani, wakilin Iran na musamman kan Syria, da Saud al-Sati, mataimakin ministan harkokin wajen Saudiyya kan harkokin siyasa, a yayin da suke magana kan yadda ake samun sauyin yanayi a kasar Siriya, da kuma mafi girman tasirin hare-haren da Isra’ila ke kaiwa a yankin.

M. Sheibani ya sake jaddada goyon bayan Iran ga hadin kai da ‘yancin kai na Siriya, yana mai yin tir da hare-haren da gwamnatin Isra’ila ke kai wa a matsayin barna da kuma tada zaune tsaye.

Ya jaddada cewa irin wadannan ayyuka na kawo cikas ga zaman lafiyar yankin da kuma saba ka’idojin kasa da kasa.

A nasa bangaren, al-Sati ya yi na’am da wannan ra’ayi, yana mai tabbatar da daidaiton matsayin Saudiyya na goyon bayan tabbatar da yankin Siriya, zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya yi Allah wadai da hare-haren da gwamnatin kasar ke kai wa a yankin na Syria, yana mai bayyana bukatar bin dokokin kasa da kasa da mutunta ikon kasa a duniya.

Bangarorin biyu sun amince da muhimmancin ci gaba da tuntubar juna dangane da ci gaban yankin, tare da jaddada bukatar yin hadin gwiwadon tinkarar kalubalen da ake fuskanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alƙaluman sakamakon jarabawar bana — JAMB
  • Ghana ta ci tarar ministoci saboda rashin bayyana kadarorin da suka mallaka
  • Iran da Saudiyya sun jaddada bukatar kare hurimin kasar Siriya
  • Bayern Munich Ta Lashe Gasar Bundesliga Ta Bana
  • Abin da ya hana ni cika alƙawarin da na yi wa ma’aikata — Gwamnan Sakkwato
  • HKI Ta Tabbatar Da Halakar Sojojinta 2 A Yankin Rafa Na Zirin Gaza
  • OPEC+ Zata Kara Yawan Man Fetur Da Take Haka Da Ganga 411,000 A Cikin Watan Yuli Mai Zuwa
  • Ayatullah Khamenei: Babu Abinda ya fi hadin kai mahimmanci ga al’ummar musulmi
  • Sarki Sanusi 16 Ya Yi Sabbin Nadade A Kano
  • Nijeriya Ta Yi Asarar Naira Biliyan 118 Sakamakon Barnatar Da Iskar Gas A Watanni 2