Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
Published: 30th, March 2025 GMT
Shugaban Karamar Hukumar Jahun dake Jihar Jigawa, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam ya kaddamar da rabon kayan sallah da kuma kudin dinki ga al’ummar yankin.
A jawabinsa wajen bikin da aka gudanar a garin Jahun, shugaban Karamar Hukumar yace Hakimai na gundumomin Jahun da Aujara da Gunka da Kadawawa da Limaman masalatan juma’a 79 na yankin za su amfana da kayan sallah da kuma kudin dinki.
Jamilu Muhammad Danmalam ya bayyana rashin Jin dadinsa bisa yadda ake mantawa da iyayen kasa da Malaman Addini a irin wannan lokacin da ya kamata a taimake su.
Ya ce yana daya daga cikin kudurorinsa na shigo da kowanne bangare na al’umma cikin tsarin shugabancinsa dan kowa ya anfana.
Danmalam ya ce a wannan wata na Ramadan karamar hukumar ta tallafawa masu bukata ta musamman da marayu da masu karamin karfi da shugabannin jam’iyyar APC da ma’aikatan gwamnati da kuma mata da maza.
Ya kara da cewar kowanne hakimi ya sami dinkin sallah na shadda mai dauke da shakwara da jamfa da wando, hade da kudin abincin sallah.
A jawabin sa, daya daga cikin limaman yankin Mallam Yahuza Gabari yace a tarihin Karamar Hukumar Jahun ba’a taba samun shugaban da ya kula da limamai da shugabannin al’umma irin shugaban Karamar Hukumar na yanzu ba.
Wasu daga cikin wadanda suka anfana da tallafin sun yabawa shugaban Karamar Hukumar bisa tagomashin da suka samu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Kayan Sallah shugaban Karamar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare
Shugaban ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a fannin cewa, ako da yaushe, kofar Hukumar ta NPA, bode take domin hadaka wacce ta zarce ta gudanar da baje koli.
Dakta Dantsoho ya kara da cewa, an samar da tsarin na EPT domin a tabbatar da cewa, ana fitar da kaya zuwa waje, ta hanyar yin amfani da na’urar zamani.
“Wannan na zai taimaka matuka wajen kaucewa samun jinkiri da kuma mai-maita aiki da Hukumar ta saba fuskanta a baya,” A cewar Dantsoho.
Kazalika, Dantsoho ya bayyana cewa, domin a samu sauki wajen kai kaya a tsakanin masu kananan da matsakaitan sana’oi, musamman duba da cewa, tsarin na EPT, zai taimaka matuka ga guraren da ake adana kaya a cikin kasar na, da kuma hada karfi da karfe da Hukumar Bunkasa Harkokin Fitar da Kayayyaki ta Kasa NEPC da sauran abokan hadaka.
“Domin Hukumar ta NPA ta gudnar da ayyukanta daidai da tsarin Gwamnatin Tarayya na samar da sauki ga yin kasuwanci, musamman duba da taken baje kolin na ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, Hukumar NPA ta samar da tsarin samar da sauki wajen bai wa ‘yan kasuwar kasar yadda za su rinka fitar da kayansu, zuwa ketare,”. Inji Dantsoho.
Shugaban ya kara da cewa, Hukumar ta kuma nasara a tsarinta na NSW, musamman duba da yadda aka samu saduwa da sauran masu ruwa da tsaki, wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci
Dantsoho ya jinjinawa mahukunta Cibiyar ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, musamman kan yadda suke ci gaba da gudanar da hada-hara kasuwanci da yanyo abokan kasuwanci na cikin gida Nijeriya, da kuma na kasashen waje, wanda hakan ya kara taimakawa, wajen habaka tattalin arzikin kasar.
Shugaban ya yi nuni da cewa, duba da yadda jihar ta Enugu ta kasance a yankin Kudu Maso Gabas, hakan zai taimaka mata wajen samar da damar kara fadada fitar da kaya zuwa ketare.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp